< Fitowa 23 >

1 “Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada kuma ku haɗa baki da mugayen mutane har da ku zama munafukai ta wurin ba da shaidar ƙarya.
“You must not spread stories that are lies. You must not help bad people by giving evidence that's malicious.
2 “Kada ku yi abin da ba daidai ba, don galibin mutane suna yin haka. Sa’ad da kuke ba da shaida a gaban shari’a, kada ku ba da shaidar ƙarya a kauce wa gaskiya don ku faranta wa taron jama’a rai.
Don't follow the crowd in doing wrong. When you give evidence in a lawsuit, don't corrupt justice by siding with the majority.
3 Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari’a.
Don't show favoritism to poor people in their legal cases either.
4 “In ka ga saniyar abokin gābanka, ko jakinsa ya ɓace, ka yi ƙoƙari ka mai da shi wurinsa.
If you come across your enemy's ox or donkey that has wandered off, take it back it to him.
5 In ka ga jakin wani maƙiyinka ya fāɗi a ƙarƙashin kayan da ya ɗauka, kada ka bar shi can, ka yi ƙoƙari ka taimake shi.
If you see the donkey of someone who hates you that has fallen under its load, don't just leave it there. You must stop and help.
6 “Kada ku kāsa yin adalci ga matalauci a wurin shari’a.
You must not prevent the poor from getting justice in their lawsuits.
7 Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi tare da mai adalci, gama ba zan bar mugun yă tafi haka kawai ba.
Don't have anything to do with making false accusations. Don't kill the innocent or those who do right, for I won't let the guilty go unpunished.
8 “Kada ka karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta waɗanda suke gani, yakan kuma karkatar da maganar masu adalci.
Don't accept bribes, for a bribe blinds those who can see, and undermines the evidence of the honest.
9 “Kada ka zalunci baƙo, ku kanku kun san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a Masar.
Don't abuse foreigners living among you, since you know very well what it's like to be foreigners, for you were once foreigners in Egypt.
10 “Shekara shida za ku nome gonakinku ku girbe amfanin gonar,
Six years you are to sow your land and harvest crops,
11 amma a shekara ta bakwai za ku bar ƙasa tă huta. Sa’an nan matalautan da suke cikinku za su sami abinci daga cikinta, namun jeji kuma za su ci abin da aka bari. Ku yi haka da gonakinku na inabi, da na itatuwan zaitun.
but in the seventh year you are to let it rest and leave it uncultivated, so that poor people may eat what grows naturally from the field and the wild animals can finish what's left. Follow the same procedure for your vineyards and olive groves.
12 “Kwana shida za ku yi aikinku, amma a rana ta bakwai, kada ku yi aiki, saboda saniyarku da jakinku su huta, haka kuma bawan da aka haifa a gidanku, da kuma baƙon da yake a cikinku yă wartsake.
You have six days to do your work, but on the seventh day you must stop working, so that your ox and your donkey can rest, and your slaves' families can catch their breath, as well as the foreigners living among you.
13 “Ku mai da hankali, ku yi biyayya da duk abin da na faɗa muku. Kada ku kira sunaye waɗansu alloli; kada a ji su a bakinku.
Make sure to pay attention to everything I've told you. Don't think to call on the names of other gods—you must not even mention them.
14 “Sau uku a shekara za ku yi mini biki.
Three times every year you are to celebrate a feast dedicated to me.
15 “Ku yi Bikin Burodi Marar Yisti, kwana bakwai za ku ci burodi marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Ku yi wannan a lokacin da aka ayana a watan Abib, gama a watan ne kuka fito daga Masar. “Kada wani yă zo a gabana hannu wofi.
You are to observe the Festival of Unleavened Bread as I instructed you. You are to eat bread without yeast for seven days at the appropriate time in the month of Abib, because that was the month you left Egypt. No one can come before me without bringing an offering.
16 “Ku yi Bikin Girbi da nunan fari na amfanin shuke-shuken gonarku. “Ku yi Bikin Tattarawa a ƙarshen shekara, sa’ad da kuka tattara amfani daga gonarku.
You are also to observe the Festival of Harvest when you present the firstfruits of the produce from what you've sown in the fields. Lastly you are to observe the Festival of Gathering-In the Harvest at the end of the year, when you gather in the harvest of the rest of your crops from the field.
17 “Sau uku a shekara, maza duka za su bayyana a gaban Ubangiji Mai Iko Duka.
Every Israelite male is to come before the Lord God at these three times every year.
18 “Kada ku miƙa mini hadayar jini tare da wani abu mai yisti. “Ba za a bar kitsen bikin hadayata yă kwana ba.
You must not offer the blood of my sacrifices together with anything that contains yeast, and the fat from the offerings presented at my festival must not be left until morning.
19 “Dole ne ku kawo mafi kyau daga nunan fari na gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a cikin madarar mahaifiyarsa.
Bring the best firstfruits of your crops to the house of the Lord your God. Don't cook a young goat in its mother's milk.
20 “Ga shi, zan aika mala’ika a gabanku, yă tsare ku a tafiyarku, yă kuma kawo ku wurin da na shirya.
Look, I'm sending an angel ahead of you to protect you on the way and to take you to the place I've prepared for you.
21 Ku saurare shi, ku kuma kasa kunne ga abin da yake faɗa. Kada ku yi masa tawaye; ba zai gafarta tawayenku ba, gama shi wakilina ne.
Make sure you pay attention to him and do what he says. Don't oppose him, because he won't forgive rebellion, for he carries my authority.
22 In kun kasa kunne sosai ga abin da yake faɗi, kuka kuma yi abin da na faɗa, zan zama magabci ga abokan gābanku, zan kuma yi hamayya da abokan hamayyanku.
However, if you listen to him carefully, and do everything that I tell you, then I will be an enemy to your enemies and I will fight those who fight against you.
23 Mala’ikana zai sha gabanku, yă kawo ku cikin ƙasar Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan’aniyawa, da Hiwiyawa, da kuma Yebusiyawa, zan kuma kawar da su.
For my angel will go ahead of you and take you into the land of the Amorites, Hittites, Perizzites, Canaanites, Hivites, and Jebusites, and I will wipe them out.
24 Kada ku durƙusa wa allolinsu, ko ku yi musu sujada, ko kuma ku bi al’adunsu. Za ku hallaka dukan allolinsu, ku kuma farfasa keɓaɓɓun duwatsunsu.
You must not bow down to their gods or worship them or follow their pagan practices. No, you must demolish their idols and smash their sacred pillars into pieces.
25 Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, albarkansa kuwa za tă kasance a kan abincinku da ruwan shanku. Zan ɗauke cuta daga cikinku.
You are to worship the Lord your God, and he will bless your food and water. I will make sure none of you fall sick.
26 A ƙasarku, mace ba za tă yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai.
No woman will have a miscarriage or be without children. I will make sure you live long lives.
27 “Zan aiki razanata a gabanku, in kuma sa ruɗami a cikin kowace al’ummar da za ku sadu da ita. Zan sa duk abokan gābanku su juye da baya, su gudu.
I will send terror about me ahead of you which will throw every nation you meet into panic. I will make all your enemies turn and run away.
28 Zan aiki rina a gabanku, su kori Hiwiyawa, Kan’aniyawa da kuma Hittiyawa.
I will send hornets ahead of you to drive out before you the Hivites and Canaanites and Hittites.
29 Amma ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar tă zama kufai har namun jeji su fi ƙarfinku.
I will not drive them out in just one year, because the land would become desolate and you would have to deal with increased numbers of wild animals.
30 Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku yă kai yadda za ku mallaki ƙasar.
Bit by bit I will drive them out ahead of you, until there are enough of you to take possession of the land.
31 “Zan kafa iyakokinku daga Jan Teku zuwa Bahar Rum, daga hamada kuma zuwa Kogi. Zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kuwa kore su daga gabanku.
I will fix your borders from the Red Sea to the Sea of the Philistines, and from the desert to the Euphrates River. I will hand the inhabitants of the land over to you, and you will drive them out.
32 Kada ku ƙulla yarjejjeniya da su, ko da allolinsu.
You must not make any agreement with them or with their gods.
33 Kada ku bari su zauna a cikin ƙasarku, in har kuka bar su, za su ɓata ku da zunubinsu na bautar allolinsu, har zai yă zama muku tarko.”
They must not be allowed to stay in your land, otherwise they will lead you to sin against me. For if you worship their gods, they will definitely become a trap for you.”

< Fitowa 23 >