< Fitowa 22 >

1 “In mutum ya saci saniya ko tunkiya ya yanka, ko ya sayar, zai biya shanu biyar, a maimakon saniyar da ya sata, ko kuma tumaki huɗu, maimakon tunkiyar da ya sata.
Аще же кто украдет телца или овцу, и заколет или продаст, пять телцев да воздаст за телца и четыри овцы за овцу.
2 “In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga yă yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa daga wurin kowa ba;
Аще же в подкопании обрящется тать, и язвен умрет, несть ему убийство:
3 amma in ya faru bayan wayewar gari, to, za a nemi alhakin jinin ɓarawon a hannun wanda ya bugi ɓarawon. “Ɓarawon da aka kama da abin da ya sata, dole yă yi cikakkiyar ramuwa, amma in ba shi da kome, dole a sayar da shi a biya abin da ya sata.
аще же взыдет солнце над ним, повинен есть, умрет за него: аще же не имать имения, да продастся за татьбу:
4 In an sami dabbar, ko saniya, ko jaki, ko tunkiya da ya sata da rai a hannunsa, dole ɓarawon yă biya taran da za a ci shi, sau biyu na kowane ɗaya.
аще же ят будет, и обрящется в руце его украденое от осляте до овцы живо, сугубо да отдаст я.
5 “In mutum ya sa dabbobinsa su yi kiwo a fili ko a gonar inabi, ya kuma bar dabbobinsa suka yi ɓarna a cikin gonar wani, sai a sa mai dabbar yă biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka.
Аще же кто потравит ниву или виноград, и пустит скот свой пастися на чужей ниве, да даст от нивы своея по плоду его: аще же всю ниву потравит, лучшая нивы своея и лучшая винограда своего да отдаст.
6 “In gobara ta tashi, ta kuma bazu cikin ƙayayyuwa, har ta cinye tarin hatsi, ko hatsin da ke tsaye, ko dukan gonar, dole wanda ya sa wutar, yă biya taran da aka yanka masa saboda ɓarnan da wutar ta yi.
Аще же изшед огнь обрящет терние и запалит гумно, или класы, или ниву, да отдаст, иже возже огнь.
7 “In mutum ya ba maƙwabcinsa azurfa, ko kaya ajiya, aka kuma sace su daga gidan maƙwabcin, in an kama ɓarawon, sai ɓarawon yă biya abin da ya sata har sau biyu.
Аще же кто даст другу сребро или сосуд сохранити, и украдется из дому мужа того, аще обрящется украдый, да воздаст сугубо:
8 Amma in ba a sami ɓarawon ba, sai wanda aka yi ajiyar a gidansa, yă bayyana a gaban alƙalai a bincika ko yana da hannu a kan kayan maƙwabcinsa.
аще же не обрящется украдый, да приидет господин дому пред бога и да кленется, яко поистинне не слукавствова он о всем положении дружнем.
9 A kowane rikicin cin amana da zai shiga tsakanin mutum biyu, ko a kan bijimi, ko jaki, ko tunkiya, ko riga, kai, ko a kan kowane irin abin da ya ɓata, da ma abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin a gaban alƙalai. Wanda alƙali ya ce shi ne mai laifi, sai yă biya ɗayan taran da za a yanka, har sau biyu.
По всей реченней неправде, о теляти и о осляти и о овце, и о ризе и о всей гибели нанесенней, что убо ни было бы, пред богом да приидет суд обоих, и обвиненный богом да отдаст сугубо ближнему.
10 “In mutum ya ba da jaki, ko saniya, ko tunkiya, ko kowace dabba wa maƙwabcinsa ajiya, sai abin ya mutu, ko ya ji rauni, ko an ɗauke shi, in ba shaida,
Аще же кто даст другу осля или телца, или овцу, или всяк скот хранити, и умрет или погибнет, или пленено будет, и никтоже увесть,
11 rantsuwa ce za tă raba tsakaninsu a gaban Ubangiji cewa babu hannunsa a dukiyar maƙwabcinsa. Mai dukiyar kuwa zai yarda da rantsuwar, ba za a bukaci wanda aka bai wa amanar yă biya ba.
клятва да будет Божия между обоими, яко поистинне не слукавствова он о всем ближняго положении, и тако приимет господин его, и да не отдаст:
12 Amma idan satan dabbar ce aka yi, dole wanda aka bai wa ajiyar yă biya mai dabbar taran da aka ci masa.
аще же украдено будет от него, да отдаст господину:
13 In naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shaida, ba za a kuwa sa maƙwabcin yă biya abin da naman jeji ya kashe ba.
аще же зверь снеде, да ведет его на звероядину, и не отдаст:
14 “In mutum ya yi aron dabba daga wurin maƙwabcinsa, sai dabbar ta ji rauni ko ta mutu, yayinda mai shi ba ya nan, dole wanda ya yi aron dabbar yă biya.
аще же кто испросит у друга, и погибнет, или умрет, или пленится, господин же его не будет с ним, отдаст:
15 Amma idan mai dabbar yana a wurin, wanda ya karɓa aron, ba zai biya kome ba. In an yi hayar dabbar ce, to, kuɗin da aka biya na hayar zai zama a madadin rashin.
аще же господин его будет с ним, да не отдаст: аще же наемник есть, да будет ему вместо мзды его.
16 “Idan mutum ya ruɗe budurwa, wadda ba wanda yake nemanta, ya kuma kwanta da ita, dole yă biya kuɗin aurenta, za tă kuma zama matarsa.
Аще же прельстит кто не обручену девицу, и будет с нею, веном да отвенит ю, (и поймет ю) себе в жену:
17 In mahaifinta ya ƙi yă ba da ita ga mutumin, dole mutumin yă biya dukiya daidai da abin da akan biya domin budurwai.
аще же возбраняя возбранит и не восхощет отец ея дати ю ему в жену, сребро да воздаст отцу, елико есть вено девическо.
18 “Kada ku bar maiya da rai.
Волхвом живым быти не попустите.
19 “Duk mutumin da ya yi jima’i da dabba dole a kashe shi.
Всякаго со скотом бывающа смертию убиете его.
20 “Duk wanda ya yi hadaya ga wani allah ban da Ubangiji, dole a hallaka shi.
Иже жертву приносит богом, смертию да потребится, но точию Господу единому.
21 “Kada a wulaƙanta, ko a zalunci baƙo, domin dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.
И пришелца не озлобите, ниже оскорбите его: пришелцы бо бесте в земли Египетстей.
22 “Kada ku ci zalin gwauruwa, ko maraya.
Всякия вдовы и сироты не озлобите:
23 In kuka yi haka, idan kuma suka yi kuka gare ni, zan ji kukansu.
аще же злобою озлобите Я, и возстенавше возопиют ко мне, слухом услышу глас их
24 Zan husata, in kuma kashe ku da takobi; matanku kuma, su ma su zama gwauraye,’ya’yanku kuwa su zama marayu.
и разгневаюся яростию, и побию вы мечем, и будут жены вашя вдовы, и чада ваша сироты.
25 “In kun ba wa jama’ata matalauta da suke tsakaninku bashin kuɗi, kada ku zama kamar masu ba da rance; kada ku sa yă biya da ruwa.
Аще же даси сребро взаем брату нищему иже у тебе, не буди его понуждаяй, ниже наложиши ему лихвы.
26 In kun ɗauki mayafi maƙwabcinku a matsayin jingina, ku mayar masa kafin fāɗuwar rana,
И аще заложит в залог ризу друг твой, до захождения солнца отдаси ему:
27 domin mayafin ne abin da yake da shi na rufe jikinsa. To, da me zai rufu yă yi barci? Sa’ad da ya yi mini kuka, zan ji, gama ni mai tausayi ne.
есть бо сия покровение ему, сия едина риза стыдения его, в чем спати будет: аще убо возопиет ко Мне, услышу его: милостив бо есмь.
28 “Kada ku yi maganar saɓo ga Allah, ko ku la’anta mai mulkin mutanenku.
Богов да не злословиши и князю людий твоих да не речеши зла.
29 “Kada ku jinkirta fitar da zakarku daga rumbunanku, ko harajin kayan da kuka saya. “Dole ku ba ni’ya’yan farinku maza.
Начатки от гумна и от точила твоего да не косниши принести (Мне): первенцы сынов твоих да даси Мне:
30 Ku yi haka da shanunku da tumakinku. Bari su kasance da iyayensu mata, har kwana bakwai, amma ku ba ni su a rana ta takwas.
тако сотвориши телцу твоему, и овце твоей, и ослу твоему: седмь дний да будет у матери, в осмый же день да отдаси оное Мне.
31 “Za ku kasance mutanena masu tsarki. Saboda kada ku ci naman da namun jeji suka kashe; ku jefa wa karnuka.
Люди святи будете Ми, и мяса звероядиннаго да не снесте, псом повержете е.

< Fitowa 22 >