< Fitowa 20 >

1 Sai Allah ya faɗi waɗannan kalmomi ya ce,
Then God spake all these wordes, saying,
2 “Ni ne Ubangiji Allahnka, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
I am the Lord thy God, which haue brought thee out of the land of Egypt, out of the house of bondage.
3 “Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli ba sai ni.
Thou shalt haue none other Gods before me.
4 Ba za ka yi wa kanka waɗansu alloli a siffar wani abu a sama a bisa, ko a ƙarƙashin ƙasa, ko a ƙarƙashin ruwa ba.
Thou shalt make thee no grauen image, neither any similitude of things that are in heauen aboue, neither that are in the earth beneath, nor that are in the waters vnder the earth.
5 Ba za ka durƙusa gare su, ko ka yi musu sujada ba. Gama ni, Ubangiji Allahnka mai kishi ne, nakan hukunta’ya’ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina,
Thou shalt not bowe downe to them, neither serue them: for I am the Lord thy God, a ielous God, visiting the iniquitie of the fathers vpon the children, vpon the third generation and vpon the fourth of them that hate me:
6 amma ina nuna ƙauna ga tsara dubbai na waɗanda suke ƙaunata, suke kuma kiyaye umarnaina.
And shewing mercie vnto thousandes to them that loue me, and keepe my commandemets.
7 Ba za ka yi amfani da sunan Ubangiji Allahnka a banza ba, gama Ubangiji zai hukunta duk wanda ya mai da sunansa banza.
Thou shalt not take the Name of the Lord thy God in vaine: for the Lord will not hold him guiltles that taketh his Name in vayne.
8 Ka tuna da ranar Asabbaci domin ka kiyaye ta da tsarki.
Remember the Sabbath day, to keepe it holy.
9 Kwana shida za ka yi dukan aikinka,
Sixe dayes shalt thou labour, and doe all thy worke,
10 amma rana ta bakwai Asabbaci ne ga Ubangiji, Allahnka. A ranar ba za ka yi wani aiki ba, ko kai, ko ɗanka, ko’yarka, ko bawa, ko baiwa, ko dabbarka, ko baƙon da yake zama tare da kai.
But the seuenth day is the Sabbath of the Lord thy God: in it thou shalt not do any worke, thou, nor thy sonne, nor thy daughter, thy man seruant, nor thy mayde, nor thy beast, nor thy stranger that is within thy gates.
11 Gama kwana shida Ubangiji ya halicci sama da ƙasa, da teku, da duk abin da yake cikinsu, amma ya huta a rana ta bakwai. Saboda haka Ubangiji ya albarkaci ranar Asabbaci, ya kuma mai da ita mai tsarki.
For in sixe dayes the Lord made the heauen and the earth, the sea, and all that in them is, and rested the seuenth day: therefore the Lord blessed the Sabbath day, and hallowed it.
12 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka.
Honour thy father and thy mother, that thy dayes may be prolonged vpon the land, which the Lord thy God giueth thee.
13 Ba za ka yi kisankai ba.
Thou shalt not kill.
14 Ba za ka yi zina ba.
Thou shalt not commit adulterie.
15 Ba za ka yi sata ba.
Thou shalt not steale.
16 Ba za ka ba da shaidar ƙarya a kan maƙwabcinka ba.
Thou shalt not beare false witnes against thy neighbour.
17 Ba za ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka ba. Ba za ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka ba, ko bawansa, ko baiwarsa, ko sansa, ko jakinsa, ko duk abin da yake na maƙwabcinka ba.”
Thou shalt not couet thy neighbours house, neither shalt thou couet thy neighbours wife, nor his man seruant, nor his mayde, nor his oxe, nor his asse, neyther any thing that is thy neighbours.
18 Da mutane suka ga tsawa da walƙiya, suka ji karar ƙaho, suka kuma ga dutsen yana hayaƙi, sai suka yi rawar jiki don tsoro. Suka tsaya da nisa
And all the people sawe the thunders, and the lightnings, and the sound of the trumpet, and the mountaine smoking and when the people saw it they fled and stoode afare off,
19 suka ce wa Musa, “Ka yi magana da mu da kanka, za mu kasa kunne. Amma kada Allah ya yi mana magana, don kada mu mutu.”
And sayde vnto Moses, Talke thou with vs, and we will heare: but let not God talke with vs, lest we die.
20 Musa ya ce wa mutane, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo don yă gwada ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.”
Then Moses sayde vnto the people, Feare not: for God is come to proue you, and that his feare may be before you, that ye sinne not.
21 Sa’ad da mutane suka tsattsaya da nesa, sai Musa ya matsa kusa da girgije mai duhu, inda Allah yake.
So the people stoode afarre off, but Moses drew neere vnto the darkenes where God was.
22 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa wannan. ‘Kun gani da kanku cewa na yi magana da ku daga sama.
And the Lord sayde vnto Moses, Thus thou shalt say vnto the children of Israel, Ye haue seene that I haue talked with you from heauen.
23 Kada ku yi waɗansu alloli in ban da ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa ko na zinariya.
Ye shall not make therefore with me gods of siluer, nor gods of golde: you shall make you none.
24 “‘Ku yi mini bagaden ƙasa, ku kuma miƙa mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, za ku hadayar da tumakinku da awakinku da shanu. Duk inda na sa a girmama sunana, zan zo wurinku, in sa muku albarka.
An altar of earth thou shalt make vnto me, and thereon shalt offer thy burnt offerings, and thy peace offerings, thy sheepe, and thine oxen: in all places, where I shall put the remembrance of my Name, I will come vnto thee, and blesse thee.
25 In kuka yi mini bagade dutse, kada ku gina shi da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama inda guduma ta taɓa duwatsun, sun haramtu ke nan.
But if thou wilt make mee an altar of stone, thou shalt not buylde it of hewen stones: for if thou lift vp thy toole vpon them, thou hast polluted them.
26 Kada ku gina wa bagadena matakala, domin kada yayinda wani yana hawa, mutane su ga tsiraicinsa.’
Neither shalt thou goe vp by steppes vnto mine altar, that thy filthines be not discouered thereon.

< Fitowa 20 >