< Fitowa 11 >

1 To, fa, sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan ƙara kawo annoba guda a kan Fir’auna da kan Masar. Bayan haka, zai bar ku, ku fita daga nan. Sa’ad da ya yi haka kuwa, zai kore ku gaba ɗaya.
Now the Lord had saide vnto Moses, yet will I bring one plague more vpon Pharaoh, and vpon Egypt: after that, he will let you go hence: when he letteth you goe, he shall at once chase you hence.
2 Ka faɗa wa mutane cewa dukan maza da mata, su roƙi maƙwabtansu kayan azurfa da na zinariya.”
Speake thou nowe to the people, that euery man require of his neighbour, and euery woman of her neighbour iewels of siluer and iewels of gold.
3 (Ubangiji ya sa mutane suka sami tagomashi a idon Masarawa, Musa kuwa ya sami girma sosai a cikin ƙasar Masar a gaban fadawan Fir’auna da kuma a gaban jama’ar.)
And the Lord gaue the people fauour in the sight of the Egyptians: also Moses was very great in the land of Egypt, in the sight of Pharaohs seruantes, and in the sight of the people.)
4 Saboda haka Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Wajen tsakar dare, zan ratsa dukan Masar.
Also Moses sayde, Thus sayth the Lord, About midnight will I goe out into the middes of Egypt.
5 Kowane ɗan fari, namiji, a Masar zai mutu, daga kan ɗan fari na Fir’auna wanda zai ci gadon sarauta, har zuwa kan ɗan fari na baiwa, wadda take niƙa, da kuma dukan’yan farin shanu.
And all the first borne in the lande of Egypt shall die, from the first borne of Pharaoh that sitteth on his throne, vnto the first borne of the maide seruant, that is at the mille, and all the first borne of beastes.
6 Za a yi kuka mai zafi ko’ina a Masar, irin wadda ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a ƙara yi ba.
Then there shalbe a great crie throughout all the land of Egypt, such as was neuer none like, nor shalbe.
7 Amma a cikin Isra’ilawa, ba karen da zai yi haushi wa mutum ko dabba.’ Ta haka za ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masar da Isra’ila.
But against none of ye children of Israel shall a dogge moue his tongue, neyther against man nor beast, that ye may knowe that the Lord putteth a difference betweene the Egyptians and Israel.
8 Dukan fadawan nan naka za su zo wurina, suna fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama’arka!’ Sa’an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir’auna a husace.
And all these thy seruants shall come downe vnto me, and fal before me, saying, Get thee out, and all the people that are at thy feete, and after this will I depart. So he went out from Pharaoh very angry.
9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir’auna zai ƙi kasa kunne gare ka, sai na ƙara aikata waɗansu mu’ujizai cikin Masar.”
And the Lord saide vnto Moses, Pharaoh shall not heare you, that my wonders may bee multiplied in the land of Egypt.
10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu’ujizai a gaban Fir’auna, amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa ba.
So Moses and Aaron did all these wonders before Pharaoh: but the Lord hardened Pharaohs heart, and he suffred not the children of Israel to goe out of his lande.

< Fitowa 11 >