< Fitowa 1 >

1 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isra’ila maza, waɗanda suka tafi Masar tare da Yaƙub; kowanne da iyalinsa.
Et voici les noms des fils d'Israël venus en Egypte avec Jacob; ils vinrent chacun avec sa maison:
2 Ruben, Simeyon, Lawi da Yahuda;
Ruben, Siméon, Lévi et Juda;
3 Issakar, Zebulun da Benyamin;
Issaschar, Zabulon et Benjamin;
4 Dan da Naftali; Gad da Asher.
Dan et Nephthali; Gad et Asser;
5 Zuriyar Yaƙub duka sun kai mutum saba’in. Yusuf ya riga ya kasance a Masar.
et toutes les personnes issues des entrailles de Jacob étaient au nombre de soixante-dix âmes; or Joseph était en Egypte.
6 Yanzu Yusuf da dukan’yan’uwansa da kuma dukan tsaran nan da suka tafi Masar, sun mutu,
Et Joseph mourut ainsi que tous ses frères et toute cette génération-là.
7 amma Isra’ilawa sun riɓaɓɓanya, suka kuma yi ta haihuwa sosai, suka yi yawan sosai, har ƙasar ta cika da su.
Et les enfants d'Israël furent féconds et pullulèrent et se multiplièrent et s'accrurent de plus en plus, et ils remplirent le pays.
8 Sai wani sabon sarki wanda bai san Yusuf ba, ya hau sarautar Masar.
Alors il s'éleva un nouveau roi sur l'Egypte, qui ne connaissait point Joseph.
9 Ya ce wa mutanensa, “Duba Isra’ilawa sun yi yawa, sun fi ƙarfinmu.
Et il dit à son peuple: Voilà que le peuple des enfants d'Israël est plus grand et plus fort que nous:
10 Ku zo, mu yi dabara a kansu, in ba haka ba za su ƙaru fiye da haka, in kuwa yaƙi ya tashi tsakaninmu da abokan gāba, za su iya haɗa kai da abokan gāba, su yaƙe mu, su bar ƙasar.”
eh bien! opposons-lui la prudence afin qu'il n'augmente pas, et que, le cas échéant d'une guerre, il ne se joigne pas à nos ennemis pour nous combattre, puis partir du pays.
11 Saboda haka sai suka naɗa shugabannin gandu a kansu don su wahalshe su, su kuma bauta musu, suka sa su suka gina biranen Fitom da Rameses su zama biranen ajiya, domin Fir’auna.
Et l'on préposa sur lui des chefs de corvée dans le but de l'accabler sous leur faix; et il bâtit pour Pharaon des villes de dépôt, Pithom et Ramsès.
12 Amma duk da wannan ƙarin wulaƙancin da ake yi musu, su kuwa sai daɗa riɓaɓɓanya suke ta yi. Sai tsoron Isra’ilawa ya ƙaru a zuciyar Masarawa,
Mais plus on l'accablait, plus il multipliait et se propageait; et ils prirent peur des enfants d'Israël.
13 ganin haka sai Masarawa suka ƙara musu wahala.
Et les Égyptiens firent peser sur les enfants d'Israël une servitude oppressive,
14 Suka baƙanta wa Isra’ilawa rai da bauta mai wuya, ta wurin sa su yin tubali da yumɓu, da kuma kowace irin bauta a gonaki. A cikin dukan ayyukansu, Masarawa ba su ji tausayinsu ba ko kaɗan.
et par de rudes travaux en argile et en briques, et par tous les travaux de la campagne ils empoisonnaient leur vie, par tout l'ouvrage auquel ils les employaient tyranniquement.
15 Sai Sarkin Masar ya gaya wa ungozomomin matan Ibraniyawa, wato, su Shofra da Fuwa ya ce,
Et le roi d'Egypte parla aux sages-femmes des Hébreux, parmi lesquelles une se nommait Siphra, et une autre Puha,
16 “Sa’ad da kuke taimakon matan Ibraniyawa lokacin haihuwa, in jaririn namiji ne ku kashe shi, amma in ta mace ce, ku bar ta da rai.”
et dit: Lorsque vous accoucherez les femmes des Hébreux, et que pendant le travail vous verrez que c'est un fils, tuez-le; mais si c'est une fille, laissez-la vivre.
17 Amma ungozomomin nan masu tsoron Allah ne, ba su kuwa aikata abin da sarkin Masar ya gaya musu ba; suka bar jarirai maza su rayu.
Mais les sages-femmes craignirent Dieu et ne se conformèrent point à l'ordre du roi d'Egypte, et elles laissèrent vivre les enfants.
18 Sai sarkin Masar ya kira ungozomomin, ya tambaye su ya ce, “Don me kuka yi haka? Don me kuka bar jarirai maza su rayu?”
Alors le roi d'Egypte manda les sages-femmes et leur dit: Pourquoi avez-vous agi de la sorte et laissé vivre les enfants?
19 Ungozoman suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Ai, matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gwarzaye ne, sukan haihu kafin ungozomomin su kai wurinsu.”
Et les sages-femmes répondirent à Pharaon: C'est que les femmes des Hébreux ne sont pas comme les Egyptiennes, car elles sont vigoureuses, et, avant l'arrivée de la sage-femme, elles ont déjà enfanté.
20 Saboda haka Allah ya nuna alheri wa ungozomomin, Isra’ilawa kuwa suka yi yawa fiye da dā.
Et Dieu fit du bien aux sages-femmes, et le peuple se multiplia et s'accrut beaucoup.
21 Saboda ungozomomin suna tsoron Allah, sai Allah ya ba su iyalan kansu.
Et parce que les sages femmes avaient eu la crainte de Dieu, Dieu leur éleva des maisons.
22 Sai Fir’auna ya ba da umarni wa mutanensa ya ce, “Duk yaron da yake namijin da haka haifa, dole ku jefa shi cikin kogi, amma ku bar yara mata su rayu.”
Alors Pharaon prescrivit cet ordre à tout son peuple: Vous jetterez au Nil tous les fils qui naîtront, mais vous laisserez vivre les filles.

< Fitowa 1 >