< Mai Hadishi 3 >

1 Akwai lokaci domin kowane abu, da kuma lokaci domin kowane aiki a duniya.
All things have their season, and in their times all things pass under heaven.
2 Lokacin haihuwa da lokacin mutuwa, lokacin shuki da lokacin tumɓukewa.
A time to be born and a time to die. A time to plant, and a time to pluck up that which is planted.
3 Lokacin kisa da lokacin warkarwa, lokacin rushewa da lokacin ginawa.
A time to kill, and a time to heal. A time to destroy, and a time to build.
4 Lokacin kuka da lokacin dariya, lokacin makoki da lokacin rawa.
A time to weep, and a time to laugh. A time to mourn, and a time to dance.
5 Lokacin warwatsa duwatsu da lokacin tara su, lokacin runguma da lokacin dainawa.
A time to scatter stones, and a time to gather. A time to embrace, and a time to be far from embraces.
6 Lokacin nema, da lokacin fid da zuciya, lokacin ajiyewa da lokacin zubarwa.
A time to get, and a time to lose. A time to keep, and a time to cast away.
7 Lokacin yagewa da lokacin ɗinkewa, lokacin yin shiru da lokacin magana.
A time to rend, and a time to sew. A time to keep silence, and a time to speak.
8 Lokacin ƙauna da lokacin ƙiyayya, lokacin yaƙi da lokacin salama.
A time of love, and a time of hatred. A time of war, and a time of peace.
9 Wace riba ce ma’aikaci yake da ita saboda wahalarsa?
What hath man more of his labour?
10 Na ga nawayar da Allah ya ɗora a kan mutane.
I have seen the trouble, which God hath given the sons of men to be exercised in it.
11 Ya yi kowane abu da kyau a lokacinsa. Ya kuma sa matuƙa a zukatan mutane, duk da haka sun kāsa gane abin da Allah ya yi daga farko zuwa ƙarshe.
He hath made all things good in their time, and hath delivered the world to their consideration, so that man cannot find out the work which God hath made from the beginning to the end.
12 Na san ba abin da ya fi wa mutane kyau fiye da su ji daɗi su kuma yi alheri yayinda suke da rai.
And I have known that there was no better thing than to rejoice, and to do well in this life.
13 Cewa kowa yă ci, yă sha, yă kuma ji daɗi cikin dukan aikinsa, wannan kyautar Allah ce.
For every man that eateth and drinketh, and seeth good of his labour, this is the gift of God.
14 Na san cewa duk abin da Allah ya yi zai dawwama har abada; ba abin da za a ƙara ko a rage. Allah ya yi haka domin mutane su girmama shi.
I have learned that all the works which God hath made, continue for ever: we cannot add any thing, nor take away from those things which God hath made that he may be feared.
15 Duk abin da yana nan ya taɓa kasancewa, kuma abin da zai kasance, ya taɓa kasancewa; Allah kuma zai nemi bayanin abubuwan da suka wuce.
That which hath been made, the same continueth: the things that shall be, have already been: and God restoreth that which is past.
16 Sai na ga wani abu kuma a duniya, a wurin shari’a, akwai mugunta a can, a wurin adalci, akwai mugunta a can.
I saw under the sun in the place of judgment wickedness, and in the place of justice iniquity.
17 Sai na yi tunani a zuciyata, “Allah zai shari’anta masu adalci da masu mugunta, gama za a kasance da lokaci domin kowane aiki, lokaci domin kowane abu.”
And I said in my heart: God shall judge both the just and the wicked, and then shall be the time of every thing.
18 Na sāke yin tunani, “Game da mutane kam, Allah kan gwada su don su san cewa ba su fi dabba ba.
I said in my heart concerning the sons of men, that God would prove them, and shew them to be like beasts.
19 Ƙaddarar mutum ɗaya take da ta dabba; ƙaddara ɗaya ce take jiransu biyu. Yadda ɗayan yake mutuwa, haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne; mutum bai fi dabba ba. Kowane abu ba shi da amfani.
Therefore the death of man, and of beasts is one, and the condition of them both is equal: as man dieth, so they also die: all things breathe alike, and man hath nothing more than beast: all things are subject to vanity.
20 Duka wuri ɗaya za su tafi; gama duka daga turɓaya suka fito, kuma ga turɓaya duka za su koma.
And all things go to one place: of earth they were made, and into earth they return together.
21 Wa ya tabbatar cewa ruhun mutum yakan tashi sama sa’an nan na dabba yă sauka ƙasa?”
Who knoweth if the spirit of the children of Adam ascend upward, and if the spirit of the beasts descend downward?
22 Saboda haka na ga babu abin da ya fi kyau wa mutum fiye da yă more wahalar aikinsa, domin wannan ne rabonsa. Gama wa zai kawo shi yă ga abin da zai faru a bayansa?
And I have found that nothing is better than for a man to rejoice in his work, and that this is his portion. For who shall bring him to know the things that shall be after him?

< Mai Hadishi 3 >