< Maimaitawar Shari’a 9 >

1 Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
Hear, Israel; you are about to cross over the Jordan today, to go in to dispossess nations greater and mightier than yourself, and cities that are great and fortified up to heaven,
2 Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
a people great and tall, the sons of the Anakim, whom you know, and of whom you have heard people say, 'Who can stand before the sons of Anak?'
3 Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
Know therefore today that Yahweh your God is he who goes over before you like a devouring fire; he will destroy them, and he will subdue them before you; so will you drive them out and make them to perish quickly, as Yahweh has said to you.
4 Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
Do not say in your heart, after Yahweh your God has thrust them out from before you, 'It was because of my righteousness that Yahweh has brought me in to possess this land,' for it was because of the wickedness of these nations that Yahweh is driving them out from before you.
5 Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
It is not because of your righteousness or the uprightness of your heart that you are going in to possess their land, but it is because of the wickedness of these nations that your God is driving them out from before you, and so that he may make come true the word that he swore to your ancestors, to Abraham, Isaac, and Jacob.
6 Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
Know therefore, that Yahweh your God is not giving you this good land to possess because of your righteousness, for you are a stubborn people.
7 Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
Remember and do not forget how you provoked Yahweh your God to anger in the wilderness; from the day that you left the land of Egypt until you came to this place, you have been rebellious against Yahweh.
8 A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
Also at Horeb you provoked Yahweh to anger, and Yahweh was angry enough with you to destroy you.
9 Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
When I went up the mountain to receive the tablets of stone, the tablets of the covenant that Yahweh made with you, I stayed on the mountain for forty days and forty nights; I neither ate bread nor drank water.
10 Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
Yahweh gave to me the two tablets of stone written with his finger; on them was written everything just like all the words that Yahweh announced to you on the mountain out of the middle of the fire on the day of the assembly.
11 A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
It happened at the end of those forty days and forty nights that Yahweh gave me the two tablets of stone, the tablets of the covenant.
12 Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
Yahweh said to me, 'Arise, go down quickly from here, for your people, whom you brought out of Egypt, have corrupted themselves. They have quickly turned aside out of the path that I commanded them. They have made for themselves a cast figure.'
13 Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
Furthermore, Yahweh spoke to me and said, 'I have seen this people; they are a stubborn people.
14 Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
Let me alone, so that I may destroy them and blot out their name from under heaven, and I will make of you a nation mightier and greater than they.'
15 Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
So I turned around and came down the mountain, and the mountain was burning. The two tablets of the covenant were in my hands.
16 Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
I looked, and behold, you had sinned against Yahweh your God. You had molded for yourselves a calf. You had quickly turned aside out of the path that Yahweh had commanded you.
17 Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
I took the two tablets and threw them out of my hands. I broke them before your eyes.
18 Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
Again I lay facedown before Yahweh for forty days and forty nights; I neither ate bread nor drank water, because of all your sin that you had committed, in doing that which was evil in the sight of Yahweh, so as to provoke him to anger.
19 Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
For I was afraid of the anger and hot displeasure with which Yahweh was angry enough against you to destroy you. But Yahweh listened to me that time also.
20 Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
Yahweh was very angry with Aaron so as to destroy him; I prayed for Aaron also at the same time.
21 Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
I took your sin, the calf that you had made, and burned it, beat it, and ground it very small, until it was as fine as dust. I threw its dust into the stream that came down from the mountain.
22 Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
At Taberah, at Massah, and at Kibroth Hattaavah, you provoked Yahweh to wrath.
23 Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
When Yahweh sent you from Kadesh Barnea and said, 'Go up and take possession of the land that I have given you,' then you rebelled against the commandment of Yahweh your God, and you did not believe or listen to his voice.
24 Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
You have been rebellious against Yahweh from the day that I knew you.
25 Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
So I lay facedown before Yahweh those forty days and forty nights, because he had said that he would destroy you.
26 Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
I prayed to Yahweh and said, 'O Lord Yahweh, do not destroy your people or your inheritance whom you have redeemed through your greatness, which you have brought out of Egypt with a mighty hand.
27 Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
Call to mind your servants Abraham, Isaac, and Jacob; do not look at the stubbornness of this people, nor at their wickedness, nor at their sin,
28 In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
so that the land from where you brought us should say, “Because Yahweh was not able to bring them into the land that he promised to them, and because he hated them, he has brought them out to kill them in the wilderness.”
29 Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”
Yet they are your people and your inheritance, whom you brought out by your great strength and by the display of your power.'

< Maimaitawar Shari’a 9 >