< Maimaitawar Shari’a 8 >

1 Ku hankali, ku bi kowane umarnin da nake ba ku a yau, saboda ku rayu, ku ƙaru, ku kuma shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku.
“All the commandments which I am entrusting to you this day, take care to observe them diligently, so that you may live and be multiplied, and so that, upon entering, you may possess the land, about which the Lord swore to your fathers.
2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku a dukan hanya, a cikin hamada waɗannan shekaru arba’in, don yă ƙasƙantar da ku, yă kuma gwada ku don yă san abin da yake a zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa, ko babu.
And you shall remember the entire journey along which the Lord your God led you, for forty years through the desert, to afflict you, and to test you, and to make known the things that were turning in your soul, whether or not you would keep his commandments.
3 Ya ƙasƙantar da ku, ya bar ku da yunwa, sa’an nan ya ciyar da ku da Manna, wadda ku, ko kakanninku, ba su sani ba, ta haka ne ya sa kuka sani cewa, ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba, amma ta wurin kowace kalmar da ta fito daga bakin Ubangiji.
He afflicted you with need, and he gave you Manna as your food, which neither you nor your fathers knew, so as to reveal to you that it is not by bread alone that man lives, but by every word that goes forth from the mouth of God.
4 Tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba a waɗannan shekaru arba’in.
Your garment, with which you were covered, has by no means decayed due to age, and your foot has not been worn down, even to this fortieth year,
5 Sai ku sani fa a cikin zuciyarku cewa kamar yadda mutum kan horar da ɗansa, haka Ubangiji Allahnku ke horar da ku.
so that you would recognize in your heart that, just as a man educates his son, so has the Lord your God educated you.
6 Ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, kuna tafiya cikin hanyoyinsa, kuna kuma girmama shi.
So may you keep the commandments of the Lord your God, and walk in his ways, and fear him.
7 Gama Ubangiji Allahnku yana fitar da ku zuwa cikin ƙasa mai kyau, ƙasa mai rafuffuka da tafkunan ruwa, tare da maɓulɓulai masu gudu a kwari da tuddai;
For the Lord your God will lead you into a good land: a land of brooks and waters and fountains, in which deep rivers burst forth from its plains and mountains,
8 ƙasa mai alkama da sha’ir, inabi da ɓaure, rumman, man zaitun da zuma;
a land of crops, barley, and vineyards, in which fig and pomegranate and olive trees spring up, a land of oil and honey.
9 ƙasa inda abinci ba zai yi ƙaranci ba, ba kuma za ku rasa kome ba; ƙasa ce inda ƙarfe ne duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta.
In that place, without any need, you shall eat your bread and enjoy an abundance of all things: where the stones are like iron, and where ore for brass is dug out of its mountains.
10 Sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda ƙasa mai kyau da ya ba ku.
So then, when you have eaten and been satisfied, you should bless the Lord your God for the excellent land which he has given to you.
11 Ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji Allahnku, har ku kāsa kiyaye umarnansa, dokokinsa da ƙa’idodinsa da nake ba ku a wannan rana ba.
Be observant and cautious, lest at some time you may forget the Lord your God, and neglect his commandments, as well as the judgments and ceremonies, which I instruct to you this day.
12 To, sa’ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sa’ad da kuka gina gidaje masu kyau, kuka zauna,
Otherwise, after you have eaten and been satisfied, and have built beautiful houses and have lived in them,
13 sa’ad da kuma garkunanku na shanu da na tumaki suka ƙaru, azurfanku da zinariyarku kuma suka ƙaru, sa’an nan dukan abin da kuke da shi ya haɓaka,
and have obtained herds of oxen, and flocks of sheep, and a plentitude of gold and silver and all things,
14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
your heart might be lifted up, and you might not remember the Lord your God, who led you away from the land of Egypt, from the house of servitude,
15 Ya bishe ku cikin hamada mai fāɗi, mai bantsoro, wannan busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa, ga macizai masu dafi da kuma kunamai. Ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara.
and who was your leader in the great and terrible wilderness, in which there was the serpent with a burning breath, and the scorpion, and the snake of thirst, and no waters at all. He led streams out of the hardest rock,
16 Ya ba ku Manna don ku ci a cikin hamada, wani abin da kakanninku ba su taɓa sani ba, don yă ƙasƙantar yă kuma gwada ku, saboda yă yi muku alheri daga baya.
and he nourished you in the wilderness with Manna, which your fathers had not known. And after he had afflicted and tested you, in the very end, he took pity on you.
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Ikona da ƙarfin hannuwana ne suka ba ni da wannan arziki.”
Otherwise, you might say in your heart: ‘My own strength, and the power of my own hand, have brought forth all these things for me.’
18 Amma ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne wanda yake ba ku azanci na yin arziki, ta haka kuwa ya tabbatar da alkawarinsa, wanda ya rantse wa kakanninku, kamar yadda yake a yau.
But remember the Lord your God, that he himself has provided you with strength, so that he may fulfill his covenant, about which he swore to your fathers, just as the present day reveals.
19 In kuka manta da Ubangiji Allahnku, kuka kuma bi waɗansu alloli, kuka yi musu sujada, kuka kuma rusuna musu, to, a yau ina gargaɗe ku cewa tabbatacce za a hallaka ku.
But if you forget the Lord your God, so that you follow foreign gods, and serve and adore them: behold, I now foretell to you that you shall utterly perish.
20 Kamar al’ummai da Ubangiji ya hallakar kafin ku, haka zai hallaka ku, domin ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku ba.
Just like the nations, which the Lord destroyed upon your arrival, so shall you also perish, if you have been disobedient to the voice of the Lord your God.”

< Maimaitawar Shari’a 8 >