< Maimaitawar Shari’a 4 >

1 To, ku ji, ya Isra’ila, ku kasa kunne ga ƙa’idodi da dokokin da nake shirin koya muku. Ku bi su domin ku yi tsawon rai, ku kuma shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji, Allahn kakanninku yake ba ku.
People of Israel, pay attention to the rules and regulations I'm teaching you to observe. That way you can stay alive, and go in and take over the country the Lord, the God of your forefathers, is giving you.
2 Kada ku ƙara, kada ku rage daga cikin abin da nake umarce ku. Amma ku kiyaye umarnan nan na Ubangiji Allahnku, da na ba ku.
You are not to add to or take away from what I'm telling you, so that you can keep the commandments of the Lord your God that I'm ordering you to follow.
3 Da idanunku, kun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba’al-Feyor. Yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka waɗansu daga cikinku waɗanda suka yi wa Ba’al-Feyor sujada,
You've seen for yourselves what the Lord did at Baal-peor where the Lord your God killed everyone among you who worshiped Baal of Peor.
4 Amma ku da kuka manne ga Ubangiji Allahnku, kuna da rai har wa yau.
Those of you who were faithful to the Lord your God are still alive today, every one of you.
5 Ga shi, na koya muku ƙa’idodi da dokoki, yadda Ubangiji Allahna ya umarce ni, don ku bi su a ƙasar da za ku shiga ku mallaki.
Listen, I have taught you the rules and regulations just as the Lord my God ordered me to do, so you can follow them in the country that you are about to enter and take over.
6 Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al’ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa’ad da al’ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, “Ba shakka, wannan babbar al’umma tana da hikima da ganewa.”
Be careful to observe them, because this will demonstrate your wisdom and insight to the other people living there who are watching. They will find out about all these rules and say, “The people of this great nation are very wise and have good insight.”
7 Wace al’umma ce mai girma haka wadda allolinta take kusa da su yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu a duk sa’ad da muka yi addu’a gare shi?
What nation is as great as us, having a god so close to them as the Lord our God is to us whenever we call on him?
8 Wace al’umma ce mai girma haka wadda take da ƙa’idodi da dokoki masu adalci kamar waɗannan ƙunshin dokokin da nake sa a gabanku a yau?
What nation is as great as us, having such good rules and regulations like all these laws that I'm placing before you today?
9 Ku kula, ku kuma lura da kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da idanunku suka gani, ko kuwa ku bari su fita daga zuciyarku muddin ranku. Ku koyar da su ga’ya’yanku, da’ya’yan’ya’yanku.
Just make sure to be very careful, and really watch what you do, so you don't forget the things you've have seen. Keep them in mind as long as you live. Teach them to your children and grandchildren.
10 Ku tuna da ranar da kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa’ad da ya ce mini, “Ka tara mutane a gabana, don su ji maganata, su koya yin mini bangirma muddin ransu a ƙasar, su kuma iya koyar da su ga’ya’yansu.”
That day when you stood in the presence of the Lord your God at Horeb, the Lord told me, “Have the people come to me and to hear what I have to say, so they may learn to have respect for me throughout their lives here on earth, and so they may teach this to their children.”
11 Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutse yayinda yana cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma baƙin gizagizai da kuma baƙin duhu.
You gathered and stood at the foot of the mountain. The mountain was on fire, shooting out flames into the sky and producing thick dark clouds.
12 Sai Ubangiji ya yi magana daga wutar. Kuka ji furcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji.
The Lord spoke to you from the fire. You heard the words, but you didn't see the form of anyone speaking—there was just a voice.
13 Ya furta alkawarinsa gare ku, Dokoki Goma, waɗanda ya umarce ku ku bi, ya kuma rubuta su a alluna biyu.
He explained to you his agreement, the Ten Commandments, which he ordered you to follow. He wrote them down on two tablets of stone.
14 Sa’an nan Ubangiji ya umarce ni a wannan lokaci, in koya muku ƙa’idodi da dokokin da za ku bi a ƙasar da kuke hayewa Urdun don mallake.
This was the time that the Lord ordered me to teach you the rules and regulations that you are to follow when you arrive in the country you're going to own once you've crossed the Jordan.
15 Ba ku ga wata siffa a ranar da Ubangiji ya yi magana da ku a Horeb daga wuta ba. Saboda haka ku lura da kanku sosai,
You didn't see any form when the Lord spoke to you from the fire at Horeb, so be very careful
16 don kada ku lalace, ku kuma yi wa kanku gunki, siffa ta wani kama, ko a kamannin namiji, ko kuwa ta mace,
that you don't spoil your relationship with the Lord by making an idol for yourselves in any shape or form, whether it looks like a male or female,
17 ko a kamannin wata dabba a duniya, ko na wani tsuntsun da yake tashi a sama,
or any land animal or bird that flies,
18 ko kuwa a kamannin wata halittar da take rarrafe a ƙasa, ko na wani kifi a cikin ruwaye a ƙarƙashi.
or of any animal that crawls on the ground or any fish in the deep sea.
19 Sa’ad da kuka ɗaga ido kuka kali sama, kuka ga rana da wata, da taurari, da dukan halittun sama, sai ku kula fa, kada ku jarrabtu, ku ce za ku yi musu sujada, ko ku bauta musu; abubuwan nan Ubangiji Allahnku ne ya rarraba wa dukan al’umman da suke ko’ina a ƙarƙashin sararin sama.
When you look up at the sky and see the sun, moon, and stars—all the heavenly bodies—don't be tempted to bow down to them. Don't worship them like all the other nations on earth in the way that the Lord has allowed.
20 Amma ku, Ubangiji ya ɗauke ku, ya fid da ku daga matuya mai narken ƙarfe, wato, daga Masar, domin ku zama jama’arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau.
Remember that the Lord took you and led you out of the iron furnace which was Egypt to be his own people, just as you are today.
21 Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, ya kuma yi rantsuwa cewa ba zan haye Urdun, in shiga ƙasan nan mai kyau da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo ba.
But the Lord was angry with me because of you, and he vowed that I wouldn't cross the Jordan to enter the good land that the Lord your God is giving you to own.
22 Zan mutu a wannan ƙasa; ba zan haye Urdun ba; amma kuna gab da ƙetarewa, ku mallaki wannan ƙasa mai kyau.
So I will not be crossing the Jordan, because I have to die here in this land. But you will cross over and occupy that good land.
23 Ku yi hankali kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku; kada fa ku yi wa kanku gunki a kamannin wani abin da Ubangiji Allahnku ya hana.
However, be careful not to forget the agreement of the Lord your God that he made with you. Don't make an idol for yourselves in the form of anything, because he has forbidden you to do this.
24 Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai ƙuna, Allah ne mai kishi.
For the Lord your God is a fire that burns everything up. He is an exclusive God.
25 Bayan kun haifi’ya’ya da jikoki, kuka kuma zauna na dogon lokaci a ƙasar, in har kuka lalace, kuka kuma yi wani irin gunki, kuna aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku, kuna kuma sa shi fushi.
After you have been living in the country for a long time and have had children and grandchildren, if you then spoil the relationship you have with the Lord and make an idol in any form. The Lord your God sees this as evil makes him angry.
26 Yau, na kira sama da duniya, su zama shaidata a kanku. Idan kuka yi rashin biyayya, lalle za ku hallaka nan da nan daga ƙasar da kuke ƙetare Urdun ku gāda. Ba za ku daɗe a cikinta ba, amma za a kawar da ku ƙaƙaf.
If you do this, I call on heaven and earth to be witnesses against you today that you will be completely wiped out from the country that you are crossing the Jordan to occupy. You will not live long there—you will be totally destroyed.
27 Ubangiji zai watsar da ku a cikin mutane, ɗan kaɗan ne kaɗai za su ragu a cikin al’umman da Ubangiji zai kai ku.
The Lord will scatter you among the other nations, and not many of you will survive in the countries where the Lord has exiled you.
28 A can za ku bauta wa allolin da mutum ya yi, na itace da dutse da ba sa gani, ba sa ji, ba sa ci, ba kuma iya sansanawa.
There you will worship gods of wood and stone made by human beings. These idols can't see or hear or eat or smell.
29 Amma daga can in kuka nemi Ubangiji Allahnku, da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku, za ku same shi.
However, if while you're there you decide to come to the Lord your God, you will find him if you come to him whole-heartedly, with complete commitment.
30 Sa’ad da kuke cikin wahala saboda waɗannan abubuwan da suka same ku nan gaba, to, sai ku juyo ga Ubangiji Allahnku, ku kuma yi masa biyayya.
When you are in trouble, after you've experienced all these things, then eventually you will return to the Lord your God and do what he says.
31 Gama Ubangiji Allahnku, Allah ne mai jinƙai; ba zai yashe ku ko yă hallaka, ko kuma yă manta da alkawarin da ya yi da kakanninku, wanda ya tabbatar da su da rantsuwa ba.
The Lord your God is a merciful God. He won't abandon you or destroy you or forget the agreement he made with your forefathers, confirmed by a solemn promise.
32 Ku bincika dukan tarihi mana, tun daga lokacin da Allah ya halicci mutane a cikin duniya har yă zuwa yanzu; ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa?
Think about it! Examine the whole of history from the beginning of time, long before you existed, when God made human beings, right up until now. Ask this question anywhere, from one end of the earth to the other: Has anything as amazing as this ever happened before; has anyone ever heard anything like this?
33 Akwai waɗansu mutanen da suka taɓa jin muryar Allah yana magana daga wuta, kamar yadda kuka ji har suka rayu?
Has a people ever heard the voice of God speaking out of the fire, like you have, and survived?
34 Akwai wani allahn da ya taɓa yin ƙoƙari yă ɗauko wa kansa wata al’umma daga wata al’umma, ta wurin gwaje-gwaje, ta wurin alamu masu banmamaki da al’ajabai, ta wurin yaƙi, ta wurin hannu mai iko, da kuma hannu mai ƙarfi, ko kuwa ta wurin ayyuka masu bangirma da na banmamaki, kamar dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi saboda ku a Masar, a kan idanunku?
Has any god tried to take a nation out of another nation and make them his own, using tests and signs and miracles and war—with his great power and incredible strength and terrifying actions—like the Lord your God did for you in Egypt, before your very eyes?
35 An nuna muku dukan waɗannan abubuwa saboda ku san cewa Ubangiji, shi ne Allah; ban da shi, babu wani.
You were shown all this so you could be certain that the Lord is God and there is no one like him.
36 Daga sama ya sa kuka ji muryarsa, don yă hore ku. A duniya ya nuna muku wutarsa mai girma, kuka kuma ji kalmominsa daga wuta.
He made you hear his voice from heaven so you would obey him. On earth he revealed himself though blazing fire, and you heard him speak to you from the fire.
37 Domin ya ƙaunaci kakanninku, ya kuma zaɓi zuriyarsu a bayansu, ya fitar da ku daga Masar ta wurin kasancewarsa da kuma ƙarfinsa mai girma,
Because he loved your forefathers, he chose you, their descendants. He himself led you out of Egypt by his great power,
38 don yă fitar da ku a gaban al’ummai da suka fi ku girma da kuma ƙarfi, ya kawo ku cikin ƙasarsu, don yă ba ku ita ta zama gādonku, kamar yadda yake a yau.
driving out ahead of you nations that were greater and stronger than you, in order to lead you to their land and give it to you as yours to own, just as you do today.
39 Ku sani, ku kuma riƙe a zuciya a wannan rana, cewa Ubangiji shi ne Allah a sama da kuma a ƙasa. Babu wani kuma.
So today be sure about this and never forget: the Lord is the only God in heaven above and on the earth below.
40 Ku kiyaye ƙa’idodi da umarnai, waɗanda nake ba ku a yau, domin zaman lafiyarku da kuma na zuriyarku bayan ba ku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.
Observe his rules and regulations that I'm giving you right now, so that you and your children will do well, and that you may have long lives in the country that the Lord your God is giving you for all time.
41 Sa’an nan Musa ya keɓe birane uku gabas da Urdun,
Then Moses assigned three sanctuary towns to the east of the Jordan
42 waɗanda duk wanda ya yi kisankai, in ba da gangan ba ne ya kashe maƙwabcinsa, wanda babu ƙiyayya tsakaninsu a dā, zai iya gudu zuwa. Zai iya gudu zuwa cikin ɗaya daga waɗannan birane, yă tsira da ransa.
where a person could run to after accidentally killing someone without deliberate hatred. To save their life they could run to one of these towns:
43 Biranen kuwa su ne, Bezer a dutsen hamada, don mutanen Ruben; Ramot Gileyad, don mutanen Gad; da kuma Golan a Bashan, don mutanen Manasse.
Bezer in the desert plain belonging to the tribe of Reuben; Ramoth in Gilead belonging to the tribe of Gad, or Golan in Bashan belonging to the tribe of Manasseh.
44 Wannan ita ce dokar da Musa ya sa a gaban Isra’ilawa.
This is the law that Moses placed before the Israelites.
45 Waɗannan su ne farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Musa ya ba su, sa’ad da suka fito daga Masar.
These are the laws, rules, and regulations Moses gave them after they had come out of Egypt.
46 Sa’ad da suke a kwari kusa da Bet-Feyor, gabas da Urdun, a ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, da Musa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi sa’ad da suka fito daga Masar.
This was when they were in the valley to the east of the Jordan near Beth-peor in the country of Sihon king of the Amorites. He had ruled from Heshbon and had been defeated by Moses and the Israelites after they had left Egypt.
47 Suka mallaki ƙasarsa da kuma ƙasar Og sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa, gabas da Urdun.
They took over his country and the country of Og king of Bashan. (They were the two kings of the Amorites who previously ruled on the east side of the Jordan.)
48 Wannan ƙasa ta tashi daga Arower a kewayen Kwarin Arnon zuwa Dutsen Siyon (wato, Hermon),
The territory went from the town of Aroer on the edge of the Arnon Valley all the way to Mount Sirion, otherwise known as Mount Hermon,
49 ya kuma haɗa da dukan Araba gabas da Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.
and included all the Arabah to the east of the Jordan down as far as the Dead Sea beside the slopes of Mount Pisgah.

< Maimaitawar Shari’a 4 >