< Maimaitawar Shari’a 32 >

1 Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
Give ear, O ye heavens, and I will speak; and hear, O earth, the words of my mouth.
2 Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
My doctrine shall drop as the rain, my speech shall distil as the dew, as the small rain upon the tender herb, and as the showers upon the grass:
3 Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
Because I will publish the name of the LORD: ascribe ye greatness unto our God.
4 Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
[He is] the Rock, his work [is] perfect: for all his ways [are] judgment: a God of truth and without iniquity, just and right [is] he.
5 Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
They have corrupted themselves, their spot [is] not [the spot] of his children: [they are] a perverse and crooked generation.
6 Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
Do ye thus requite the LORD, O foolish people and unwise? [is] not he thy father [that] hath bought thee? hath he not made thee, and established thee?
7 Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
Remember the days of old, consider the years of many generations: ask thy father, and he will shew thee; thy elders, and they will tell thee.
8 Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
When the most High divided to the nations their inheritance, when he separated the sons of Adam, he set the bounds of the people according to the number of the children of Israel.
9 Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
For the LORD’s portion [is] his people; Jacob [is] the lot of his inheritance.
10 A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
He found him in a desert land, and in the waste howling wilderness; he led him about, he instructed him, he kept him as the apple of his eye.
11 kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
As an eagle stirreth up her nest, fluttereth over her young, spreadeth abroad her wings, taketh them, beareth them on her wings:
12 Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
[So] the LORD alone did lead him, and [there was] no strange god with him.
13 Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
He made him ride on the high places of the earth, that he might eat the increase of the fields; and he made him to suck honey out of the rock, and oil out of the flinty rock;
14 da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
Butter of kine, and milk of sheep, with fat of lambs, and rams of the breed of Bashan, and goats, with the fat of kidneys of wheat; and thou didst drink the pure blood of the grape.
15 Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
But Jeshurun waxed fat, and kicked: thou art waxen fat, thou art grown thick, thou art covered [with fatness; ] then he forsook God [which] made him, and lightly esteemed the Rock of his salvation.
16 Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
They provoked him to jealousy with strange [gods], with abominations provoked they him to anger.
17 Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
They sacrificed unto devils, not to God; to gods whom they knew not, to new [gods that] came newly up, whom your fathers feared not.
18 Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
Of the Rock [that] begat thee thou art unmindful, and hast forgotten God that formed thee.
19 Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
And when the LORD saw [it], he abhorred [them], because of the provoking of his sons, and of his daughters.
20 Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
And he said, I will hide my face from them, I will see what their end [shall be: ] for they [are] a very froward generation, children in whom [is] no faith.
21 Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
They have moved me to jealousy with [that which is] not God; they have provoked me to anger with their vanities: and I will move them to jealousy with [those which are] not a people; I will provoke them to anger with a foolish nation.
22 Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
For a fire is kindled in mine anger, and shall burn unto the lowest hell, and shall consume the earth with her increase, and set on fire the foundations of the mountains. (Sheol h7585)
23 “Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
I will heap mischiefs upon them; I will spend mine arrows upon them.
24 Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
[They shall be] burnt with hunger, and devoured with burning heat, and with bitter destruction: I will also send the teeth of beasts upon them, with the poison of serpents of the dust.
25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
The sword without, and terror within, shall destroy both the young man and the virgin, the suckling [also] with the man of gray hairs.
26 Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
I said, I would scatter them into corners, I would make the remembrance of them to cease from among men:
27 Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
Were it not that I feared the wrath of the enemy, lest their adversaries should behave themselves strangely, [and] lest they should say, Our hand [is] high, and the LORD hath not done all this.
28 Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
For they [are] a nation void of counsel, neither [is there any] understanding in them.
29 A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
O that they were wise, [that] they understood this, [that] they would consider their latter end!
30 Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
How should one chase a thousand, and two put ten thousand to flight, except their Rock had sold them, and the LORD had shut them up?
31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
For their rock [is] not as our Rock, even our enemies themselves [being] judges.
32 Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
For their vine [is] of the vine of Sodom, and of the fields of Gomorrah: their grapes [are] grapes of gall, their clusters [are] bitter:
33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
Their wine [is] the poison of dragons, and the cruel venom of asps.
34 “Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
[Is] not this laid up in store with me, [and] sealed up among my treasures?
35 Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
To me [belongeth] vengeance, and recompence; their foot shall slide in [due] time: for the day of their calamity [is] at hand, and the things that shall come upon them make haste.
36 Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
For the LORD shall judge his people, and repent himself for his servants, when he seeth that [their] power is gone, and [there is] none shut up, or left.
37 Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
And he shall say, Where [are] their gods, [their] rock in whom they trusted,
38 allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
Which did eat the fat of their sacrifices, [and] drank the wine of their drink offerings? let them rise up and help you, [and] be your protection.
39 “Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
See now that I, [even] I, [am] he, and [there is] no god with me: I kill, and I make alive; I wound, and I heal: neither [is there any] that can deliver out of my hand.
40 Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
For I lift up my hand to heaven, and say, I live for ever.
41 sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
If I whet my glittering sword, and mine hand take hold on judgment; I will render vengeance to mine enemies, and will reward them that hate me.
42 Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
I will make mine arrows drunk with blood, and my sword shall devour flesh; [and that] with the blood of the slain and of the captives, from the beginning of revenges upon the enemy.
43 Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
Rejoice, O ye nations, [with] his people: for he will avenge the blood of his servants, and will render vengeance to his adversaries, and will be merciful unto his land, [and] to his people.
44 Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
And Moses came and spake all the words of this song in the ears of the people, he, and Hoshea the son of Nun.
45 Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
And Moses made an end of speaking all these words to all Israel:
46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
And he said unto them, Set your hearts unto all the words which I testify among you this day, which ye shall command your children to observe to do, all the words of this law.
47 Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
For it [is] not a vain thing for you; because it [is] your life: and through this thing ye shall prolong [your] days in the land, whither ye go over Jordan to possess it.
48 A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
And the LORD spake unto Moses that selfsame day, saying,
49 “Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
Get thee up into this mountain Abarim, [unto] mount Nebo, which [is] in the land of Moab, that [is] over against Jericho; and behold the land of Canaan, which I give unto the children of Israel for a possession:
50 A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
And die in the mount whither thou goest up, and be gathered unto thy people; as Aaron thy brother died in mount Hor, and was gathered unto his people:
51 Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
Because ye trespassed against me among the children of Israel at the waters of Meribah-Kadesh, in the wilderness of Zin; because ye sanctified me not in the midst of the children of Israel.
52 Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”
Yet thou shalt see the land before [thee; ] but thou shalt not go thither unto the land which I give the children of Israel.

< Maimaitawar Shari’a 32 >