< Maimaitawar Shari’a 3 >

1 Biye da wannan muka juya muka haura ta hanyar wajen Bashan, inda Og, sarkin Bashan tare da dukan mayaƙansa suka fito don su sadu da mu a yaƙi, a Edireyi.
پس برگشته، به راه باشان رفتیم، و عوج ملک باشان با تمامی قوم خود به مقابله مابیرون آمده، در ادرعی جنگ کرد.۱
2 Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ji tsoronsa, gama na riga na miƙa shi da dukan mayaƙansa da kuma ƙasarsa gare ka. Yi masa abin da ka yi wa Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon.”
و خداوند مراگفت: «از او مترس زیرا که او و تمامی قومش وزمینش را به‌دست تو تسلیم نموده‌ام، تا بطوری که با سیحون ملک اموریان که در حشبون ساکن بود، عمل نمودی، با وی نیز عمل نمایی.»۲
3 Saboda haka Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, sarkin Bashan da dukan mayaƙansa a hannuwanmu. Muka karkashe su, ba mu bar wani da rai ba.
پس یهوه، خدای ما، عوج ملک باشان را نیز و تمامی قومش را به‌دست ما تسلیم نموده، او را به حدی شکست دادیم که احدی از برای وی باقی نماند.۳
4 A wannan lokaci muka kwashe dukan biranensa. Babu ɗaya daga birane sittin da ba mu ɗauke daga gare su ba, dukan yankin Argob, masarautar Og a Bashan.
و در آنوقت همه شهرهایش را گرفتیم، وشهری نماند که از ایشان نگرفتیم، یعنی شصت شهر و تمامی مرزبوم ارجوب که مملکت عوج در باشان بود.۴
5 Dukan biranen nan masu katanga da suke da tsayi masu ƙofofi da ƙyamare, akwai kuma manya ƙauyukan da ba su da katanga.
جمیع اینها شهرهای حصاردار بادیوارهای بلند و دروازه‌ها و پشت بندها بود، سوای قرای بی‌حصار بسیار کثیر.۵
6 Muka hallaka su ƙaƙaf, kamar yadda muka yi wa Sihon sarkin Heshbon, muka hallaka kowace birni, maza, mata da yara.
و آنها رابالکل هلاک کردیم، چنانکه با سیحون، ملک حشبون کرده بودیم، هر شهر را با مردان و زنان واطفال هلاک ساختیم.۶
7 Amma dukan dabbobin da kuma ganimar daga biranensu muka kwaso wa kanmu.
و تمامی بهایم و غنیمت شهرها را برای خود به غارت بردیم.۷
8 A lokacin ne muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato, ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga Kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon.
و در آن وقت زمین را از دست دو ملک اموریان که به آن طرف اردن بودند، از وادی ارنون تا جبل حرمون، گرفتیم.۸
9 (Hermon ne Sidoniyawa suke kira Siriyon, Amoriyawa kuwa suna kira shi Senir.)
(و این حرمون راصیدونیان سریون می‌خوانند و اموریان آن راسنیر می‌خوانند. )۹
10 Muka kama dukan biranen da suke kan tudu, da dukan Gileyad, da dukan Bashan, har zuwa Saleka da Edireyi, biranen masarautar Og a Bashan.
تمام شهرهای هامون وتمامی جلعاد و تمامی باشان تا سلخه و ادرعی که شهرهای مملکت عوج در باشان بود.۱۰
11 (Og sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu cikin Refahiyawa. An yi gadonsa da ƙarfe, tsawon gadon ya fi ƙafa goma sha uku, fāɗinsa kuwa ƙafa shida ne. Yana nan a Rabba ta Ammonawa har yanzu.)
زیرا که عوج ملک باشان از بقیه رفائیان تنها باقی‌مانده بود. اینک تخت خواب او تخت آهنین است آیاآن در ربت بنی عمون نیست. و طولش نه ذراع وعرضش چهار ذراع برحسب ذراع آدمی می‌باشد.۱۱
12 Cikin ƙasar da muka kwasa a lokacin, na ba wa mutanen Ruben da mutanen Gad yankin arewa na Arower ta Kwarin Arnon, haɗe da rabin ƙasar tudu ta Gileyad, tare da biranenta.
و این زمین را در آن وقت به تصرف آوردیم، و آن را از عروعیر که برکنار وادی ارنون است و نصف کوهستان جلعاد؛ و شهرهایش را به روبینیان و جادیان دادم.۱۲
13 Sai kuma na ba wa rabin kabilar Manasse sauran rabin ƙasar tudu ta Gileyad da kuma dukan Bashan, masarautar Og (Wato, dukan yankin ƙasan nan na Argob a Bashan da dā ake kira ƙasar Refahiyawa.
و بقیه جلعاد و تمامی باشان را که مملکت عوج باشد به نصف سبطمنسی دادم، یعنی تمامی مرزبوم ارجوب را باتمامی باشان که زمین رفائیان نامیده می‌شود.۱۳
14 Yayir na zuriyar Manasse ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawwot Yayir.)
یائیر بن منسی تمامی مرزبوم ارجوب را تا حدجشوریان و معکیان گرفت، و آنها را تا امروز به اسم خود باشان، حووت یائیر نامید.۱۴
15 Na kuma ba da Gileyad ga Makir.
و جلعادرا به ماکیر دادم.۱۵
16 Amma ga mutanen Ruben da mutanen Gad, na ba da yankin da ya tashi daga Gileyad, ya gangara zuwa Kwarin Arnon (tsakiyar kwarin kuwa shi ne iyaka) ya fita zuwa Kogin Yabbok, wanda yake shi ne iyakar Ammonawa.
و به روبینیان و جادیان، ازجلعاد تا وادی ارنون، هم وسط وادی و هم کناره‌اش تا وادی یبوق را که حد بنی عمون باشد، دادم.۱۶
17 Iyakarsa daga yamma kuwa shi ne Urdun a Araba, daga Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri) a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas.
و عربه را نیز و اردن و کناره‌اش را ازکنرت تا دریای عربه که بحرالملح باشد، زیردامنه های فسجه به طرف مشرق دادم.۱۷
18 Na umarce ku a lokacin na ce, “Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban’yan’uwanku, Isra’ilawa.
و در آن وقت به شما امر فرموده، گفتم: «یهوه خدای شما این زمین را به شما داده است تاآن را به تصرف آورید، پس جمیع مردان جنگی شما مهیا شده، پیش روی برادران خود، بنی‌اسرائیل، عبور کنید.۱۸
19 Amma matanku, yaranku da dabbobinku (na sani kuna da dabbobi masu yawa), su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku,
لیکن زنان و اطفال ومواشی شما، چونکه می‌دانم مواشی بسیار دارید، در شهرهای شما که به شما دادم، بمانند.۱۹
20 sai Ubangiji ya ba da hutu ga sauran’yan’uwanku, yadda ya yi da ku, su ma suka sami ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su, a ƙetaren Urdun, sa’an nan kowannenku zai komo ga mallakar da na ba ku.”
تاخداوند به برادران شما مثل شما آرامی دهد، وایشان نیز زمینی را که یهوه خدای شما به آنطرف اردن به ایشان می‌دهد، به تصرف آورند، آنگاه هریکی از شما به ملک خود که به شما دادم، برگردید.»۲۰
21 A lokacin nan na umarci Yoshuwa na ce, “Da idanunka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan sarakuna biyu. Haka Ubangiji zai yi da dukan masarautai a can, inda za ku.
و در آن وقت یوشع را امر فرموده، گفتم: «هرآنچه یهوه، خدای شما، به این دوپادشاه کرده است، چشمان تو دید، پس خداوندبا تمامی ممالکی که بسوی آنها عبور می‌کنی، چنین خواهد کرد.۲۱
22 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku zai yi yaƙi dominku.”
از ایشان مترسید زیرا که یهوه خدای شماست که برای شما جنگ می‌کند.»۲۲
23 A lokacin, na roƙi Ubangiji na ce,
و در آنوقت نزد خداوند استغاثه کرده، گفتم:۲۳
24 “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka fara nuna wa bawanka ɗaukakarka da ikonka. Akwai wani allah a sama ko a duniya, wanda zai aikata waɗannan manyan ayyukan kamar ka?
«ای خداوند یهوه تو به نشان دادن عظمت و دست قوی خود به بنده ات شروع کرده‌ای، زیرا کدام خداست در آسمان یا در زمین که مثل اعمال و جبروت تو می‌تواند عمل نماید.۲۴
25 Ina roƙonka, bari in ƙetare in ga ƙasa mai kyau ɗin nan a ƙetaren Urdun, wannan ƙasar mai kyau ta tuddai, da kuma Lebanon.”
تمنا اینکه عبور نمایم و زمین نیکو را که به آنطرف اردن است و این کوه نیکو و لبنان را ببینم.»۲۵
26 Amma saboda ku, Ubangiji ya yi fushi da ni, bai kuwa saurare ni ba. Sai Ubangiji ya ce, “Ya isa haka, kada ka ƙara yin magana da ni game da wannan batu.
لیکن خداوند بخاطر شما با من غضبناک شده، مرا اجابت ننمود و خداوند مرا گفت: «تو را کافی است. بار دیگر درباره این امر با من سخن مگو.۲۶
27 Haura zuwa ƙwanƙolin Fisga, ka dubi ƙasar da idanunka daga kowane gefe, yamma, da arewa, da kudu, da kuma gabas, gama ba za ka ƙetare wannan Urdun ba.
به قله فسجه برآی و چشمان خود را به طرف مغرب و شمال و جنوب و مشرق بلند کرده، به چشمان خود ببین، زیرا که از این اردن نخواهی گذشت.۲۷
28 Amma ka umarci Yoshuwa, ka ƙarfafa shi, ka kuma ba shi ƙarfin gwiwa, gama shi ne zai jagoranci wannan mutane su haye, yă kuma ba su gādon ƙasar da za ka gani.”
اما یوشع را امر فرموده، او را دلیر وقوی گردان، زیرا که او پیش این قوم عبور نموده، زمینی را که تو خواهی دید، برای ایشان تقسیم خواهد نمود.»۲۸
29 Sai muka zauna a kwari kusa da Bet-Feyor.
پس در دره، در برابر بیت فغورتوقف نمودیم.۲۹

< Maimaitawar Shari’a 3 >