< Maimaitawar Shari’a 27 >

1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
Or Moïse et les Anciens d'Israël commandèrent au peuple, en disant: Gardez tous les commandements que je vous prescris aujourd'hui.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
C'est qu'au jour que tu auras passé le Jourdain pour entrer au pays que l'Eternel ton Dieu te donne, tu te dresseras de grandes pierres, et tu les enduiras de chaux;
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
Puis tu écriras sur elles toutes les paroles de cette Loi, quand tu auras passé, afin que tu entres au pays que l'Eternel ton Dieu te donne, qui est un pays découlant de lait et de miel; ainsi que l'Eternel, le Dieu de tes pères, t'[en] a parlé.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
Quand donc vous aurez passé le Jourdain, vous dresserez ces pierres-là sur la montagne de Hébal, selon que je vous le commande aujourd'hui, et vous les enduirez de chaux.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
Tu bâtiras aussi là un autel à l'Eternel ton Dieu, un autel, [dis-je], de pierres, sur lesquelles tu ne lèveras point le fer.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
Tu bâtiras l'autel de l'Eternel ton Dieu de pierres entières, et sur cet [autel] tu offriras des holocaustes à l'Eternel ton Dieu.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
Tu y offriras aussi des sacrifices de prospérités, et tu mangeras là, et te réjouiras devant l'Eternel ton Dieu.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
Et tu écriras sur ces pierres-là toutes les paroles de cette loi, en les exprimant bien nettement.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
Et Moïse et les Sacrificateurs, qui sont de la race de Lévi, parlèrent à tout Israël, en disant: Ecoute et entends, Israël, tu es aujourd'hui devenu le peuple de l'Eternel ton Dieu.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
Tu obéiras donc à la voix de l'Eternel ton Dieu et tu feras ces commandements et ces statuts que je te prescris aujourd'hui.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
Moïse commanda aussi en ce jour-là au peuple, en disant:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
Ceux-ci se tiendront sur la montagne de Guérizim pour bénir le peuple, quand vous aurez passé le Jourdain, [savoir] Siméon, Lévi, Juda, Issacar, Joseph, et Benjamin;
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
Et ceux-ci, Ruben, Gad, Aser, Zabulon, Dan, et Nephthali, se tiendront sur la montagne de Hébal, pour maudire.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
Et les Lévites prendront la parole, et diront à haute voix à tous les hommes d'Israël:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit l'homme qui fera une image taillée, ou de fonte, car c'est une abomination à l'Eternel, l'ouvrage des mains d'un ouvrier, et qui la mettra dans un lieu secret; et tout le peuple répondra, et dira: Amen.
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui aura méprisé son père, ou sa mère; et tout le peuple dira: Amen.
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui transporte les bornes de son prochain; et tout le peuple dira: Amen.
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui fait égarer l'aveugle dans le chemin; et tout le peuple dira: Amen.
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui fait injustice à l'étranger, à l'orphelin, et à la veuve; et tout le peuple dira: Amen.
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui couche avec la femme de son père; car il découvre le pan de la robe de son père; et tout le peuple dira: Amen.
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui couche avec une bête; et tout le peuple dira: Amen.
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui couche avec sa sœur, fille de son père, ou fille de sa mère; Et tout le peuple dira: Amen.
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui couche avec sa belle-mère; et tout le peuple dira: Amen.
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui frappe son prochain en secret; et tout le peuple dira: Amen.
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui prend quelque présent pour mettre à mort l'homme innocent; et tout le peuple dira: Amen.
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
Maudit soit celui qui ne persévère point dans les paroles de cette Loi, pour les faire; et tout le peuple dira: Amen.

< Maimaitawar Shari’a 27 >