< Maimaitawar Shari’a 25 >

1 Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
If cause is bitwixe ony men, and thei axen iugis, thei schulen yyue the victorie of riytfulnesse to him, whom thei perseyuen to be iust, thei schulen condempne hym of wickidnesse, whom thei perseyuen to be wickid.
2 in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
Sotheli if thei seen hym that synnede, worthi of betyngis, thei schulen caste him doun, and make to be betun bifor hem; also the maner of betyngis schal be for the mesure of synne,
3 amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
so oneli that tho passe not the noumbre of fourti, lest thi brother be to-rent viliche bifore thin iyen, and go awei.
4 Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
Thou schalt not bynde the `mouth of the oxe tredynge thi fruytis in the corn floor.
5 In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
Whanne britheren dwellen to gidere, and oon of hem is deed with out fre children, the wijf of the deed brother schal not be weddid to anothir man, but his brothir schal take hir, and schal reise seed of his brother.
6 Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
And he schal clepe the firste gendrid sone `of hir bi the name `of hym, `that is, of the deed brothir, that his name be not don awei fro Israel.
7 Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
Forsothe if he nyle take the wijf of his brother, which is due to hym bi lawe, the womman schal go to the yate of the citee; and sche schal axe the grettere men in birthe, and sche schal seie, `The brother of myn hosebonde nyle reise seed of his brother in Israel, nethir wole take me in to mariage.
8 Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
And anoon thei schulen make hym to be clepid, and thei schulen axe. If he answerith, Y nyle take hir to wijf;
9 sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
the womman schal go to hym bifor the eldre men of Israel, and sche schal take awei the schoo, and sche schal spete in to his face, and schal seie, So it schal be doon to the man, that bildith not `the hows of his brother;
10 Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
and `the name of hym schal be clepid in Israel, The hows of the man vnschood.
11 In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
If twei men han strijf bitwixe hem silf, and oon bigynneth to stryue ayens another, and the wijf of `the tother man wole delyuere hir hosebonde fro the hond of the strongere man, and puttith hond, and `takith the schamefast membris `of hym,
12 sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
thou schalt kitte awei `the hond of hir, nether thou schalt be bowid on hir bi ony mercy.
13 Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Thou schalt not haue in the bagge dyuerse weiytis,
14 Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
a grettere and a lesse, nether a buyschel more and lesse schal be in thin hows.
15 Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Thou schalt haue a iust weiyte and trewe, and an euene buyschel `and trewe schal be to thee, that thou lyue in myche tyme on the lond which thi Lord God schal yyue to thee.
16 Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
For the Lord schal haue hym abhomynable that doith these thingis, and he wlatith, `ethir cursith, al vnriytfulnesse.
17 Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
Haue thou mynde what thingis Amalech dide to thee in the weie, whanne thou yedist out of Egipt;
18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
hou he cam to thee, and killide the laste men of thin oost, that saten wery, whanne thou were disesid with hungur and trauel, and he dredde not God.
19 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!
Therfor whanne thi Lord God hath youe reste to thee, and hath maad suget alle naciouns `bi cumpas, in the lond which he bihiyte to thee, thou schalt do awei `the name of hym vndur heuene; be thou war lest thou foryete.

< Maimaitawar Shari’a 25 >