< Maimaitawar Shari’a 17 >

1 Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
“You shall not immolate to the Lord your God a sheep or an ox, in which there is a blemish or any defect at all; for this is an abomination to the Lord your God.
2 In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
When there will have been found among you, within one of your gates which the Lord your God will give to you, a man or a woman who is doing evil in the sight of the Lord your God, and who is transgressing his covenant,
3 wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
so as to go and serve foreign gods and adore them, such as the sun and the moon, or any of the host of heaven, which I have not instructed,
4 in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
and when this will have been reported to you, and, upon hearing it, if you have inquired diligently and have found it to be true, that the abomination is being done in Israel:
5 sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
you shall lead forward the man or the woman who has perpetrated this most wicked thing to the gates of your city, and they shall be stoned to death.
6 Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
By the mouth of two or three witnesses, he who is to be put to death shall perish. Let no one be killed with only one person speaking testimony against him.
7 Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
First, the hands of the witnesses shall be upon him who will be put to death, and lastly, the hands of the remainder of the people shall be sent forth. So may you take away the evil from your midst.
8 In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
If you have perceived that there is among you a difficult and doubtful matter of judgment, between blood and blood, cause and cause, leprosy and leprosy, and if you will have seen that the words of the judges within your gates vary: rise up and ascend to the place which the Lord your God will choose.
9 Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
And you shall approach the priests of the Levitical stock, and the judge, who shall be among them at that time, and you shall inquire of them, and they will reveal to you the truth of the judgment.
10 Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
And you shall accept whatever they will say, those who preside in the place which the Lord will choose, and whatever they will teach you,
11 Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
in accord with his law, and you shall follow their sentence. Neither shall you turn aside to the right or to the left.
12 Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
But whoever will be arrogant, unwilling to obey the order of the priest who ministers at that time to the Lord your God, and the decree of the judge, that man shall die. And so shall you take away the evil from Israel.
13 Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
And when the people hear about this, they shall be afraid, so that no one, from that time on, will swell with pride.
14 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
When you will have entered into the land which the Lord your God will give to you, and you possess it, and you live in it, and you say, ‘I will appoint a king over me, just as all the surrounding nations have done,’
15 ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
you shall appoint him whom the Lord your God will choose from among the number of your brothers. You cannot make a man of another people king, one who is not your brother.
16 Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
And when he will have been appointed king, he shall not multiply horses for himself, nor lead the people back into Egypt, having been exalted by the number of his horsemen, especially since the Lord has instructed you never to return along the same way.
17 Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
He shall not have many wives, who might allure his mind, and he shall not have immense weights of silver and gold.
18 Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
Then, after he has been seated upon the throne of his kingdom, he shall write for himself the Deuteronomy of this law in a volume, using a copy from the priests of the Levitical tribe.
19 Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
And he shall have it with him, and he shall read it all the days of his life, so that he may learn to fear the Lord his God, and to keep his words and ceremonies, which are instructed in the law.
20 don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.
And so may his heart not become exalted with arrogance over his brothers, nor turn aside to the right or to the left, so that he and his sons may reign for a long time over Israel.”

< Maimaitawar Shari’a 17 >