< Maimaitawar Shari’a 1 >

1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
These are the words which Moses spoke to all Israel beyond the Jordan in the wilderness, in the Arabah over against Suph, between Paran, and Tophel, and Laban, and Hazeroth, and Dizahab.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
It is eleven days' journey from Horeb by the way of Mount Seir to Kadesh Barnea.
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
It happened in the fortieth year, in the eleventh month, on the first day of the month, that Moses spoke to the children of Israel, according to all that YHWH had given him in commandment to them;
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
after he had struck Sihon the king of the Amorites, who lived in Heshbon, and Og the king of Bashan, who lived in Ashtaroth and in Edrei.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
Beyond the Jordan, in the land of Moab, began Moses to declare this law, saying,
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
"YHWH our God spoke to us in Horeb, saying, You have lived long enough in this mountain:
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
turn, and take your journey, and go to the hill country of the Amorites, and to all the places near there, in the Arabah, in the hill country, and in the lowland, and in the Negev, and by the sea coast, the land of the Canaanites, and Lebanon, as far as the great river, the river Perath.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Look, I have set the land before you: go in and possess the land which I swore to your fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give to them and to their descendants after them."
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
I spoke to you at that time, saying, "I am not able to bear you myself alone:
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
YHWH your God has multiplied you, and look, you are this day as the stars of the sky for multitude.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
YHWH, the God of your fathers, make you a thousand times as many as you are, and bless you, as he has promised you.
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
How can I myself alone bear your encumbrance, and your burden, and your strife?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
Take wise men of understanding and well known according to your tribes, and I will make them heads over you."
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
You answered me, and said, "The thing which you have spoken is good to do."
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
So I took the heads of your tribes, wise men, and known, and made them heads over you, captains of thousands, and captains of hundreds, and captains of fifties, and captains of tens, and officers, according to your tribes.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
I commanded your judges at that time, saying, "Hear cases between your brothers, and judge righteously between a man and his brother, and the foreigner who is living with him.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
You shall not show partiality in judgment; you shall hear the small and the great alike; you shall not be afraid of the face of man; for the judgment is God's. The case that is too hard for you, you shall bring to me, and I will hear it."
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
I commanded you at that time all the things which you should do.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
We traveled from Horeb, and went through all that great and terrible wilderness which you saw, by the way to the hill country of the Amorites, as YHWH our God commanded us; and we came to Kadesh Barnea.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
I said to you, "You have come to the hill country of the Amorites, which YHWH our God gives to us.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
Look, YHWH your God has set the land before you: go up, take possession, as YHWH, the God of your fathers, has spoken to you; do not be afraid, neither be dismayed."
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
You came near to me everyone of you, and said, "Let us send men before us, that they may search the land for us, and bring us word again of the way by which we must go up, and the cities to which we shall come."
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
The thing pleased me well; and I took twelve men of you, one man for every tribe:
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
and they turned and went up into the hill country, and came to the Valley of Eshcol, and spied it out.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
They took of the fruit of the land in their hands, and brought it down to us, and brought us word again, and said, "It is a good land which YHWH our God gives to us."
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
Yet you wouldn't go up, but rebelled against the commandment of YHWH your God:
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
and you murmured in your tents, and said, "Because YHWH hated us, he has brought us forth out of the land of Egypt, to deliver us into the hand of the Amorites, to destroy us.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Where are we going up? Our brothers have made our heart to melt, saying, 'The people are greater and taller than we; the cities are great and fortified up to the sky; and moreover we have seen the sons of the Anakim there.'"
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
Then I said to you, "Do not dread, neither be afraid of them.
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
YHWH your God who goes before you, he will fight for you, according to all that he did for you in Egypt before your eyes,
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
and in the wilderness, where you have seen how that YHWH your God bore you, as a man does bear his son, in all the way that you went, until you came to this place."
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Yet in this thing you did not believe YHWH your God,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
who went before you in the way, to seek you out a place to pitch your tents in, in fire by night, to show you by what way you should go, and in the cloud by day.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
YHWH heard the voice of your words, and was angry, and swore, saying,
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
"Surely not one of these men of this evil generation shall see the good land, which I swore to give to your fathers,
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
except Caleb the son of Jephunneh: he shall see it; and to him will I give the land that he has trodden on, and to his children, because he has wholly followed YHWH."
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
Also YHWH was angry with me for your sakes, saying, "You also shall not go in there:
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
Joshua the son of Nun, who stands before you, he shall go in there. Encourage him, because he will cause Israel to inherit it.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
Moreover your little ones, whom you said should be a prey, and your children, who this day have no knowledge of good or evil, they shall go in there, and to them will I give it, and they shall possess it.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
But as for you, turn, and take your journey into the wilderness by the way to the Red Sea."
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
Then you answered and said to me, "We have sinned against YHWH our God, we will go up and fight, according to all that YHWH our God commanded us." Every man of you put on his weapons of war, and presumed to go up into the hill country.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
YHWH said to me, "Tell them, 'Do not go up, neither fight; for I am not among you; lest you be struck before your enemies.'"
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
So I spoke to you, and you did not listen; but you rebelled against the commandment of YHWH, and were presumptuous, and went up into the hill country.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
The Amorites, who lived in that hill country, came out against you, and chased you, as bees do, and beat you down in Seir, even to Hormah.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
You returned and wept before YHWH; but YHWH did not listen to your voice, nor gave ear to you.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
So you stayed in Kadesh many days, according to the days that you remained.

< Maimaitawar Shari’a 1 >