< Amos 9 >

1 Na ga Ubangiji yana tsaye a gaban bagade, ya kuma ce, “Bugi kan ginshiƙan don madogaran ƙofa su girgiza. Saukar da su a kan dukan mutane; waɗanda ba su mutu ba zan kashe su da takobi. Ba mutum guda da zai tsere, babu wani da zai tsira.
I saw the Lord towering above the altar, and he commanded: Strike the tops of the pillars so that the foundations may shake, bring them down on the heads of the people below. The rest of them I will slay with the sword: no one will get away, no one will escape.
2 Ko da sun tona rami kamar zurfin kabari, daga can hannuna zai fitar da su. Ko da sun hau can sama daga can zan sauko da su. (Sheol h7585)
If they dig down to Sheol, there will my hand take them. If they climb up to the heavens, from there will I bring them down. (Sheol h7585)
3 Ko da sun ɓuya a bisa Karmel, a can zan farauce su in cafko. Ko da sun ɓuya can ƙarƙashin teku, a can zan umarci maciji yă sare su.
If they hide themselves on the top of Carmel, there will I search them out and take them. If they hide out of my sight at the bottom of the sea, there will I command the sea serpent to bite them.
4 Ko da abokan gābansu sun kore su zuwa zaman bauta, a can zan umarci takobi yă kashe su. “Zan sa musu ido don mugunta ba don alheri ba.”
If they are taken into captivity by their enemies, there will I command the sword to slay them. I will keep my eye on them but for evil and not for good.
5 Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, shi da yakan taɓa ƙasa sai ta narke, kuma dukan mazauna cikinta suna makoki, ƙasar gaba ɗaya takan hau ta kuma sauka kamar Nilu, sa’an nan ta nutse kamar kogin Masar,
It is the Lord the God of hosts, who touches the earth and it trembles, all who live on it mourn. The earth rises up like the Nile, and sinks like the Nile of Egypt.
6 shi da ya gina kyakkyawar fadarsa a cikin sammai ya kuma kafa harsashenta a duniya, shi da yakan kira ruwan teku yă kuma kwarara su a bisa duniya, Ubangiji ne sunansa.
The one who builds in the heavens, who sets the dome of the sky over the earth, who summons the waters of the sea and pours them out on the face of the earth: the Lord is his name.
7 “Ku ba Isra’ilawa ba ne, daidai gare ni kamar yadda Kushawa suke?” In ji Ubangiji. “Ban fito da Isra’ila daga Masar ba, Filistiyawa kuma daga Kaftor Arameyawa kuma daga Kir ba?
To me, Israelites, you are just like the Cushites, says the Lord. Yes, I brought Israel up out of the land of Egypt, but also the Philistines from Caphtor, and the Arameans from Kir!
8 “Tabbatacce idanun Ubangiji Mai Iko Duka suna a kan mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka shi daga fuskar duniya, duk da haka ba zan hallaka gidan Yaƙub ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji.
Behold the eyes of the Lord God are on the sinful kingdom: I will destroy it from the face of the earth! But I will not completely destroy the house of Jacob, says the Lord.
9 “Gama zan ba da umarni, zan kuma tankaɗe gidan Isra’ila a cikin dukan ƙasashe kamar yadda ake tankaɗe hatsi a cikin matankaɗi kuma ko ƙwaya ɗaya ba za tă fāɗi a ƙasa ba.
For behold I am about to give the command, and I will shake the house of Israel among all the nations just as one shakes grain in a sieve, but not a pebble shall fall to the ground.
10 Dukan masu zunubi a cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, wato, su masu cewa, ‘Masifa ba za tă fāɗo ko ta same mu ba.’
All the sinners of my people, who deny that disaster will touch or befall them, will die by the sword.
11 “A wannan rana zan maido da tentin Dawuda da ya fāɗi. Zan gyaggyara wuraren da suka yayyage, in kuma maido da kufansa in gina shi kamar yadda yake a dā,
On that day I will raise up the fallen house of David, I will wall up its gaps and raise up its ruins, I will rebuild it as it was long ago.
12 domin su mallaki raguwar Edom da duk al’ummai da suke amsa sunana,” in ji Ubangiji shi wanda zai yi waɗannan abubuwa.
They will possess again the rest of Edom, and all the nations which once you ruled for me, says the Lord, who will do this.
13 “Ranaku suna zuwa, in ji Ubangiji, “sa’ad da mai huɗa zai sha gaban mai girbi mai shuki kuma yă bi bayan mai matsin inabi. Sabon ruwan inabi zai ɗiga daga duwatsu yă kuma kwararo daga tuddai.
Listen! The days are coming, says the Lord, when the harvest is too big to reap before it is time to plough, when the grapes cannot be all trod before it is time to sow, when the mountains will run with sweet wine, and every hill will flow with it.
14 Zan dawo da waɗanda aka kai zaman bauta mutanena Isra’ila. “Za su sāke gina biranen da suke kango su kuma zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi su kuma sha ruwan inabinsu; za su yi lambuna su kuma ci amfaninsu.
I will bring back my people Israel, they will rebuild waste cities and inhabit them, plant vineyards and drink their wine, make gardens and eat their fruit.
15 Zan dasa Isra’ila a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumɓuke su daga ƙasar da na ba su ba,” in ji Ubangiji Allahnku.
I will plant them on their own soil, and they will never again be uprooted from their land which I have given them, says the Lord your God.

< Amos 9 >