< Amos 5 >

1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Èujte ovu rijeè, naricanje koje podižem za vama, dome Izrailjev.
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
Pade, neæe više ustati djevojka Izrailjeva; baèena je na zemlju svoju, nema nikoga da je podigne.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
Jer ovako veli Gospod Gospod: u gradu iz kojega je izlazila tisuæa ostaæe stotina, a iz kojega je izlazila stotina u njemu æe ostati deset domu Izrailjevu.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
Jer ovako veli Gospod domu Izrailjevu: tražite me, i biæete živi.
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
A ne tražite Vetilja, i ne idite u Galgal, i ne prolazite u Virsaveju, jer æe Galgal otiæi u ropstvo, a Vetilj æe se obratiti u ništa.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Tražite Gospoda i biæete živi, da ne obuzme doma Josifova kao oganj i spali i ne bude nikoga da gasi Vetilj.
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
Koji obraæate sud u pelen, i pravdu na zemlju obarate,
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
Onoga tražite koji je stvorio zvijezde kola i štape, i koji pretvara sjen smrtni u jutro a dan u tamnu noæ, koji doziva vode morske i proljeva ih po zemlji; ime mu je Gospod.
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
Koji podiže pogibao na jakoga, te pogibao doðe na grad.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
Mrze na onoga koji kara na vratima, i gade se na onoga koji govori pravo.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Zato što gazite siromaha i uzimate od njega žito u danak, sagradiste kuæe od tesana kamena, ali neæete sjedjeti u njima; nasadiste lijepe vinograde, ali neæete piti vina iz njih.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
Jer znam bezakonja vaša, kojih je mnogo, i grijehe vaše, koji su veliki, koji muèite pravednika, primate poklone i izvræete pravdu ubogima na vratima.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Zato æe pravedni muèati u ovo vrijeme, jer je zlo vrijeme.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Tražite dobro a ne zlo, da biste bili živi; i tako æe Gospod Bog nad vojskama biti s vama, kako rekoste.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Mrzite na zlo i ljubite dobro, i postavite na vratima sud, ne bi li se Gospod Bog nad vojskama smilovao na ostatak Josifov.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Zato ovako veli Gospod Bog nad vojskama, Gospod: biæe tužnjava po svijem ulicama, i po svijem putovima govoriæe: jaoh! jaoh! i zvaæe ratare na žalost i na tužnjavu one koji umiju naricati.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
I po svijem æe vinogradima biti tužnjava, jer æu proæi posred tebe, govori Gospod.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
Teško onima koji žele dan Gospodnji! što æe vam dan Gospodnji? tada je mrak a ne vidjelo.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Kao da bi ko bježao od lava pa bi ga sreo medvjed; ili kao da bi ko došao u kuæu i naslonio se rukom na zid, pa bi ga zmija ujela.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Nije li dan Gospodnji mrak a ne vidjelo? i tama, bez svjetlosti?
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
Mrzim na vaše praznike, odbacio sam ih, i neæu da mirišem svetkovina vaših.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Ako mi prinesete žrtve paljenice i prinose svoje, neæu ih primiti, i neæu pogledati na zahvalne žrtve od ugojene stoke vaše.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Ukloni od mene buku pjesama svojih, i sviranja psaltira tvojih neæu da èujem.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
Nego sud neka teèe kao voda i pravda kao silan potok.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Jeste li meni prinosili žrtve i dare u pustinji èetrdeset godina, dome Izrailjev?
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
Nego ste nosili šator Moloha svojega, i Hijuna, likove svoje, zvijezdu boga svojega, koje sami sebi naèiniste.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
Zato æu vas preseliti iza Damaska, govori Gospod, kojemu je ime Bog nad vojskama.

< Amos 5 >