< Amos 2 >

1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Så sier Herren: For tre misgjerninger av Moab, ja for fire vil jeg ikke ta det tilbake - fordi de brente Edom-kongens ben til kalk;
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
men jeg vil sende ild mot Moab, og den skal fortære Kerijots palasser, og Moab skal dø under krigsbulder, under hærskrik, under basunens lyd,
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
og jeg vil utrydde dommeren av deres land, og alle dets fyrster vil jeg drepe sammen med ham, sier Herren.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Så sier Herren: For tre misgjerninger av Juda, ja for fire vil jeg ikke ta det tilbake - fordi de foraktet Herrens lov og ikke holdt hans bud, og deres løgnguder, som deres fedre hadde fulgt, førte dem vill;
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
men jeg vil sende ild mot Juda, og den skal fortære Jerusalems palasser.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Så sier Herren: For tre misgjerninger av Israel, ja for fire vil jeg ikke ta det tilbake - fordi de selger den uskyldige for penger og den fattige for et par sko,
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
de som higer efter å se støv på de ringes hode og bøier retten for de saktmodige. En mann og hans far går til samme pike, så de vanhelliger mitt hellige navn.
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
På pantsatte klær strekker de sig ved hvert alter, og vin som de har tatt som bøter, drikker de i sin Guds hus.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
Og jeg utryddet da amorittene foran dem, de som var høie som sedertrær og sterke som eketrær, og jeg ødela deres frukt oventil og deres røtter nedentil,
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
og jeg førte eder op fra Egyptens land, og jeg ledet eder i ørkenen i firti år, forat I skulde få amorittens land til eiendom,
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
og jeg opvakte nogen av eders sønner til profeter, og nogen av eders unge menn til nasireere. Er det ikke så, I Israels barn? sier Herren.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
Men I fikk nasireerne til å drikke vin, og I forbød profetene å profetere.
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
Se, jeg vil knuge eder ned, likesom en vogn full av kornbånd knuger allting ned;
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
den raske skal intet tilfluktssted finne, og den sterke ikke kunne gjøre bruk av sin kraft, og helten ikke berge sitt liv;
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
bueskytteren skal ikke holde stand, den som er lett på foten, skal ikke berge sitt liv, og heller ikke rytteren på sin hest,
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
den modigste iblandt heltene skal flykte naken på den dag, sier Herren.

< Amos 2 >