< Ayyukan Manzanni 4 >

1 Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
А коли промовляли вони до наро́ду оце́, до них приступили священики, і вла́да сторожі храму й саддукеї,
2 Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
обурюючись, що навчають наро́д та звіщають в Ісусі воскресі́ння з мертвих.
3 Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
І руки наклали на них, і до в'язниці всадили до ра́нку, бо вже вечір настав був.
4 Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
І багато-хто з тих, хто слухав слово, увірували; число ж мужів таки́х було тисяч із п'ять.
5 Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
І сталось, що ра́нком зібралися в Єрусалимі начальники їхні, і старші та книжники,
6 Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
і Анна первосвященик, і Кайя́фа, і Іван, і Олександер, і скільки було їх із роду первосвященичого.
7 Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
І, поставивши їх посере́дині, запиталися: „Якою ви силою чи яким ви ім'я́м те робили?“
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
Тоді Петро, переповнений Духом Святим, промовив до них: „Начальники люду та старши́ни Ізраїлеві!
9 In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
Як сьогодні беруть нас на до́пит про те доброді́йство недужій люди́ні, як вона вздоро́влена, -
10 to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
нехай буде відо́мо всім вам, і всім лю́дям Ізраїлевим, що Ім'я́м Ісуса Христа Назаряни́на, що Його розп'яли́ ви, та Його воскресив Бог із мертвих, — Ним поставлений він перед вами здоровий!
11 Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
Він „камінь, що ви, будівни́чі, відкинули, але каменем став Він нарі́жним!“
12 Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
І нема ні в кім іншім спасі́ння. Бо під небом нема іншого Йме́ння, даного людям, що ним би спасти́ся ми мали“.
13 Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
А бачивши сміли́вість Петра та Івана, і спостерігши, що то люди оби́два невчені та про́сті, дивувалися, і пізнали їх, що вони з Ісусом були́.
14 Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
Та бачивши, що вздоро́влений чоловік стоїть з ними, нічого навпро́ти сказати не могли.
15 Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
І, звелівши їм вийти із синедріо́ну, зачали радитися між собою,
16 Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
говорячи: „Що́ робити нам із цими людьми́? Бож усім ме́шканцям Єрусалиму відо́мо, що вчинили вони явне чудо, і не можемо того заперечити.
17 Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
Та щоб більш не поши́рювалось це в наро́ді, то з погрозою заборонімо їм, щоб ніко́му з людей вони не говорили про Це Ім'я́“.
18 Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
І, закли́кавши їх, наказали їм не говорити, і взагалі не навчати про Ісусове Йме́ння.
19 Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
І відповіли́ їм Петро та Іван, та й сказали: „Розсудіть, чи це справедливе було б перед Богом, щоб слухатись вас більш, як Бога?
20 Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
Бо не можемо ми не казати про те, що́ ми бачили й чули!“
21 Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
А вони пригрози́ли їм ще, і відпустили їх, не знайшовши нічо́го, щоб їх покарати, через людей, бо всі сла́вили Бога за те, що сталось.
22 Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
Бо ро́ків більш сорока мав той чоловік, що на нім відбулося це чудо вздоро́влення.
23 Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
Коли ж їх відпустили, вони до своїх прибули́ й сповістили, про що́ первосвященики й старші до них говорили.
24 Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
Вони ж, вислухавши, однодушно свій голос до Бога підне́сли й промовили: „Владико, що небо, і землю, і море, і все, що в них є, Ти створив!
25 Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
Ти уста́ми Давида, Свого слуги́, отця нашого, сказав Духом Святим: „Чого люди бунтуються, а наро́ди задумують ма́рне?
26 Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
Повстають царі зе́мні, і збираються старші докупи на Господа та на Христа Його“.
27 Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
Бо справді зібралися в місці оцім проти Отрока Святого Твого Ісуса, що Його намастив Ти, Ірод та По́нтій Пилат із поганами та з наро́дом Ізраїлевим,
28 Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
учинити оте, що рука Твоя й воля Твоя наперед встановили були, щоб збуло́ся.
29 Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
І тепер споглянь, Господи, на їхні погрози, і дай Своїм рабам із повною сміли́вістю слово Твоє повіда́ти,
30 Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
коли руку Свою простягатимеш Ти на вздоро́влення, і щоб знаме́на та чуда чинились Ім'я́м Твого Святого Отрока Ісуса“.
31 Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
Як вони ж помолились, затряслося те місце, де зібрались були, і перепо́внилися всі Святим Духом, — і зачали говори́ти Слово Боже з сміли́вістю!
32 Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
А люди, що ввірували, мали серце одне й одну душу, і жоден із них не вважав що з маєтку свого́ за своє, але в них усе спі́льним було́.
33 Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
І апо́столи з вели́кою силою свідчили про воскресіння Ісуса Господа, і благода́ть велика на всіх них була!
34 Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
Бо жоден із них не терпів недостачі: бо, хто мав поле чи дім, продавали, і заплату за про́даж прино́сили,
35 su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
та й клали в ногах у апо́столів, — і роздавалося кожному, хто потре́бу в чім мав.
36 Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
Так, Йо́сип, що Варна́вою — що в перекладі є „син потіхи“— був про́званий від апо́столів, Левит, родом кі́прянин,
37 ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.
мавши поле, продав, а гроші приніс, та й поклав у ногах у апо́столів.

< Ayyukan Manzanni 4 >