< 2 Sama’ila 23 >

1 Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
Now these are the last words of David: The saying of David the son of Jesse, and the saying of the man raised on high, the anointed of the God of Jacob, and the sweet singer of Israel:
2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
The spirit of the LORD spoke by me, and His word was upon my tongue.
3 Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
The God of Israel said, The Rock of Israel spoke to me: 'Ruler over men shall be the righteous, even he that ruleth in the fear of God,
4 yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
And as the light of the morning, when the sun riseth, a morning without clouds; when through clear shining after rain, the tender grass springeth out of the earth.'
5 “Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
For is not my house established with God? for an everlasting covenant He hath made with me, ordered in all things, and sure; for all my salvation, and all my desire, will he not make it to grow?
6 Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
But the ungodly, they are as thorns thrust away, all of them, for they cannot be taken with the hand;
7 Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
But the man that toucheth them must be armed with iron and the staff of a spear; and they shall be utterly burned with fire in their place.
8 Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
These are the names of the mighty men whom David had: Josheb-basshebeth a Tahchemonite, chief of the captains; the same was Adino the Eznite; he lifted up his spear against eight hundred, whom he slew at one time.
9 Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
And after him was Eleazar the son of Dodo the son of an Ahohite, one of the three mighty men with David, when they jeoparded their lives against the Philistines that were there gathered together to battle, and the men of Israel were gone away;
10 amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
he stood firm, and smote the Philistines until his hand was weary, and his hand did cleave unto the sword; and the LORD wrought a great victory that day; and the people returned after him only to strip the slain.
11 Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
And after him was Shammah the son of Age the Ararite. And the Philistines were gathered together into a troop, where was a plot of ground full of lentils; and the people fled from the Philistines.
12 Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
But he stood in the midst of the plot, and defended it, and slew the Philistines; and the LORD wrought a great victory.
13 A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
And three of the thirty chief went down, and came to David in the harvest time unto the cave of Adullam; and the troop of the Philistines were encamped in the valley of Rephaim.
14 Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
And David was then in the stronghold, and the garrison of the Philistines was then in Beth-lehem.
15 Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
And David longed, and said: 'Oh that one would give me water to drink of the well of Beth-lehem, which is by the gate!'
16 Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
And the three mighty men broke through the host of the Philistines, and drew water out of the well of Beth-lehem, that was by the gate, and took it, and brought it to David; but he would not drink thereof, but poured it out unto the LORD.
17 Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
And he said: 'Be it far from me, O LORD, that I should do this; shall I drink the blood of the men that went in jeopardy of their lives?' therefore he would not drink it. These things did the three mighty men.
18 Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
And Abishai, the brother of Joab, the son of Zeruiah, was chief of the three. And he lifted up his spear against three hundred and slew them, and had a name among the three.
19 Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
He was most honourable of the three; therefore he was made their captain; howbeit he attained not unto the first three.
20 Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
And Benaiah the son of Jehoiada, the son of a valiant man of Kabzeel, who had done mighty deeds, he smote the two altar-hearths of Moab; he went down also and slew a lion in the midst of a pit in time of snow;
21 Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
and he slew an Egyptian, a goodly man; and the Egyptian had a spear in his hand; but he went down to him with a staff, and plucked the spear out of the Egyptian's hand, and slew him with his own spear.
22 Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
These things did Benaiah the son of Jehoiada, and had a name among the three mighty men.
23 Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
He was more honourable than the thirty, but he attained not to the first three. And David set him over his guard.
24 Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
Asahel the brother of Joab was one of the thirty; Elhanan the son of Dodo of Beth-lehem;
25 Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
Shammah the Harodite, Elika the Harodite;
26 Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
Helez the Paltite, Ira the son of Ikkesh the Tekoite;
27 Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
Abiezer the Anathothite, Mebunnai the Hushathite;
28 Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
Zalmon the Ahohite, Maharai the Netophathite;
29 Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
Heleb the son of Baanah the Netophathite, Ittai the son of Ribai of Gibeah of the children of Benjamin;
30 Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
Benaiah a Pirathonite, Hiddai of Nahale-gaash;
31 Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
Abi-albon the Arbathite, Azmaveth the Barhumite;
32 Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
Eliahba the Shaalbonite, of the sons of Jashen, Jonathan;
33 ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
Shammah the Hararite, Ahiam the son of Sharar the Ararite;
34 Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
Eliphelet the son of Ahasbai, the son of the Maacathite, Eliam the son of Ahithophel the Gilonite;
35 Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
Hezrai the Carmelite, Paarai the Arbite;
36 Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
Igal the son of Nathan of Zobah, Bani the Gadite;
37 Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
Zelek the Ammonite, Naharai the Beerothite, armour-bearer to Joab the son of Zeruiah;
38 Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite;
39 da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.
Uriah the Hittite. Thirty and seven in all.

< 2 Sama’ila 23 >