< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
E falou David ao Senhor as palavras deste cântico, no dia em que o Senhor o livrou das mãos de todos os seus inimigos e das mãos de Saul.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Disse pois: O Senhor é o meu rochedo, e o meu lugar forte, e o meu libertador.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Deus é o meu rochedo, nele confiarei: o meu escudo, e a força da minha salvação, o meu alto retiro, e o meu refúgio. O meu Salvador, de violência me salvaste.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
O Senhor, digno de louvor, invoquei, e de meus inimigos fiquei livre.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Porque me cercaram as ondas de morte: as torrentes de Belial me assombraram.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Cordas do inferno me cingiram; encontraram-me laços de morte. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Estando em angústia, invoquei ao Senhor, e a meu Deus clamei: do seu templo ouviu ele a minha voz, e o meu clamor chegou aos seus ouvidos.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Então se abalou e tremeu a terra, os fundamentos dos céus se moveram e abalaram, porque ele se irou.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Subiu o fumo de seus narizes, e da sua boca um fogo devorador: carvões se incenderam dele.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
E abaixou os céus, e desceu: e uma escuridão havia debaixo de seus pés.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
E subiu sobre um cherubim, e voou: e foi visto sobre as asas do vento.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
E por tendas pôs as trevas ao redor de si: ajuntamento de águas, nuvens dos céus.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Pelo resplendor da sua presença brasas de fogo se accendem.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Trovejou desde os céus o Senhor: e o altíssimo fez soar a sua voz.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
E disparou flechas, e os dissipou: raios e os perturbou.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
E apareceram as profundezas do mar, os fundamentos do mundo se descobriram: pela repreensão do Senhor, pelo sopro do vento dos seus narizes.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
Desde o alto enviou, e me tomou: tirou-me das muitas águas.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Livrou-me do meu possante inimigo, e daqueles que me tinham ódio, porque eram mais fortes do que eu.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Encontraram-me no dia da minha calamidade: porém o Senhor se fez o meu esteio.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
E tirou-me à largura, e arrebatou-me dali; porque tinha prazer em mim.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
Recompensou-me o Senhor conforme à minha justiça: conforme à pureza de minhas mãos me retribuiu.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Porque guardei os caminhos do Senhor: e não me apartei impiamente do meu Deus.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Porque todos os seus juízos estavam diante de mim: e de seus estatutos me não desviei.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
Porém fui sincero perante ele: e guardei-me da minha iniquidade.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
E me retribuiu o Senhor conforme à minha justiça, conforme à minha pureza diante dos seus olhos.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Com o benigno te mostras benigno: com o varão sincero te mostras sincero.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
Com o puro te mostras puro: mas com o perverso te mostras avesso.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
E o povo aflito livras: mas teus olhos são contra os altivos, e tu os abaterás.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Porque tu, Senhor, és a minha candeia: e o Senhor esclarece as minhas trevas.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Porque contigo passo pelo meio dum esquadrão: pelo meu Deus salto um muro.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
O caminho de Deus é perfeito, e a palavra do Senhor refinada; e é o escudo de todos os que nele confiam.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Porque, quem é Deus, senão o Senhor? e quem é rochedo, senão o nosso Deus?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Deus é a minha fortaleza e a minha força, e ele perfeitamente desembaraça o meu caminho.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Faz ele os meus pés como os das cervas, e me põe sobre as minhas alturas.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Instrui as minhas mãos para a peleja, de maneira que um arco de cobre se quebra pelos meus braços.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Também me deste o escudo da tua salvação, e pela tua brandura me vieste a engrandecer.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Alargaste os meus passos debaixo de mim, e não vacilaram os meus artelhos.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Persegui os meus inimigos, e os derrotei, e nunca me tornei até que os consumisse.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
E os consumi, e os atravessei, de modo que nunca mais se levantaram, mas cairam debaixo dos meus pés.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Porque me cingiste de força para a peleja, fizeste abater-se debaixo de mim os que se levantaram contra mim.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
E deste-me o pescoço de meus inimigos, daqueles que me tinham ódio, e os destruí.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Olharam, porém não houve libertador: sim, para o Senhor, porém não lhes respondeu.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Então os moí como o pó da terra; como a lama das ruas os trilhei e dissipei.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Também me livraste das contendas do meu povo; guardaste-me para cabeça das nações; o povo que não conhecia me servirá.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Os filhos de estranhos se me sujeitaram; ouvindo a minha voz, me obedeceram.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Os filhos de estranhos descairam; e, cingindo-se, sairam dos seus encerramentos.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
Vive o Senhor, e bendito seja o meu rochedo; e exaltado seja Deus, a rocha da minha salvação:
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
O Deus que me dá inteira vingança, e sujeita os povos debaixo de mim.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
E o que me tira dentre os meus inimigos: e tu me exaltas sobre os que contra mim se levantam; do homem violento me livras.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Por isso, ó Senhor, te louvarei entre as gentes, e entoarei louvores ao teu nome.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
Ele é a torre das salvações do seu rei, e usa de benignidade com o seu ungido, com David, e com a sua semente para sempre.

< 2 Sama’ila 22 >