< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
Ke LEUM GOD El molella David liki inpaol Saul ac mwet lokoalok pac saya, na David el onkakin on soko inge nu sin LEUM GOD:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
LEUM GOD El eot ku luk, nien wikla luk, Ac Mwet Lango luk.
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
God luk El mwe loang luk, Ke nga muta yorol nga inse misla. El loangeyu oana sie mwe loeyuk; El lain mwet lokoalok luk ac ase misla nu sik. El mwet lango luk; El loangeyu ac moliyula liki mwe lokoalok.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Nga pang nu sin LEUM GOD, Ac El moliyula liki mwet lokoalok luk. Kaksakin LEUM GOD!
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Noa lun misa apinyula; Noa lun kunausten toki nu fuk.
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Mwe kapir lun misa srumasryula, Ac kulyuk akola in sruokyuwi. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
In keok luk, nga pang nu sin LEUM GOD; Nga pang nu sin God luk tuh Elan kasreyu. In tempul lal el lohng pusrek; El porongo ke nga pang Elan kasreyu.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Na faclu rarrar ac usrusryak; Pwelung yen engyeng uh mukuikui ac kusrusrsrusr Mweyen God El kasrkusrak!
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Kulasr fofosryak liki infwacl, Sie e in kunausten ac mulut fol sikyak liki oalul.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
El seya acn lucng ac tufoki, Wi sie pukunyeng lohsr ye nial.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
El sohksok mui fin cherub; El pwesroul ke poun eng uh.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
El nokmulla ke lohsr; Pukunyeng matoltol sessesla ke kof raunella.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Mulut fol firiryak liki sarom su oan ye mutal.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
Na LEUM GOD El ngirngir yen engyengu me, Ac pusren God Kulana lohngyuk.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
El pisrik pisr natul, ac mwet lokoalok lal fahsrelik; Ke kalmelik lun sarom El oru elos kaingelik.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
Ke LEUM GOD El kai mwet lokoalok lal Ac ngirla nu selos ke kasrkusrak, Acn loal in meoa wanginla koano, Ac pwelung lun faclu ikakelik.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
LEUM GOD El saplaki lucng me ac sruokyuwi; El amakinyuyak liki inkof loal.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
El moliyula liki mwet lokoalok kulana luk, Ac liki elos nukewa su srungayu. Elos arulana ku likiyu.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Ke nga muta in mwe ongoiya, elos lainyu, Tusruktu LEUM GOD El loangeyula.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
El kasreyu ac srukyuyak liki mwe fosrnga; El moliyula mweyen el insewowo sik.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
LEUM GOD El ase lacnen orekma suwohs luk; El akinsewowoyeyu mweyen wangin ma koluk luk.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Nga akos na ma sap lun LEUM GOD; Nga tiana forla liki God luk.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
Nga karinganang ma sap lal nukewa, Nga tia seakos ma El sapkin.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
El etu lah wangin ma sutuu luk, Ac nga sifacna liyeyuyang tuh nga in tia oru ma koluk.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Ouinge El ase mwe mol nu sik mweyen nga oru ma suwohs, Mweyen El etu lah wangin mwetik.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
O LEUM GOD, kom oaru nu selos su oaru nu sum, Ac kom arulana wo nu selos su moul suwohs.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
Kom nasnas nu selos su nasnas, A kom kwaselos su koluk.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Kom molelos su inse pusisel, A kom akpusiselyalos su inse fulat.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
LEUM GOD, kom kalem luk; Kom sisla lohsr likiyu.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Kom akkeyeyu tuh nga in lain mwet lokoalok luk Ac ase ku nu sik in kutangla loang lalos.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Suwoswoslana orekma lun God se inge, Kas lal arulana pwaye ac fal in lulalfongiyuk! El oana sie mwe loang Nu sin mwet nukewa su suk molela sel.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
LEUM GOD mukena El God; God mukena El mwe loang lasr.
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
God se inge El nien molela ku luk; El oru inkanek luk in misla ac wo.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
El akkeye niuk in suwohs oana soko deer; El karinginyu fineol uh.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
El akpahyeyu nu ke mweun Tuh nga in ku in orekmakin mwe pisr kulana.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
O LEUM GOD, kom karinginyu ac moliyula; Kasru lom oru nga in pwengpeng.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Kom karinginyu tuh nga in tia sruoh, Ac nga soenna ikori.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Nga ukwe mwet lokoalok luk ac kutangulosla; Nga tia tui nwe ke na nga kunauselosla.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Nga srunglulosi, ac elos tia ku in tuyak; Elos kutangyukla oan ye mutuk.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Kom akkeyeyu nu ke mweun Ac ase kutangla fin mwet lokoalok luk.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Kom oru mwet lokoalok luk in kaing likiyu; Nga kunauselosla su srungayu.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Elos suk mwet in kasrelos, a wangin mwet molelosla; Elos pang nu sin LEUM GOD, a El tiana topuk.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Nga toanelosi, ac elos ekla oana kutkut; Nga itungulosi oana fohk furarrar inkanek uh.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Kom moliyula liki mwet alein nu sik, Ac oakiya tuh nga in leum fin mutunfacl uh; Mwet ma nga tia etu, inge elos orekma nu sik.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Mwetsac elos srim ye mutuk; Ke elos lohng pusrek, elos akos.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Pulaik lalos wanginla Ac elos rarrar ke elos tuku liki pot ku lalos.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
LEUM GOD El moul! Kaksakin El su nien molela luk! Fahkelik pwengpeng lun God ku su moliyula!
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
El ase kutangla fin mwet lokoalok luk; El akpusiselye mutunfacl su muta ye kolyuk luk
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Ac moliyula liki mwet lokoalok luk. O LEUM GOD, kom ase kutangla fin mwet lokoalok luk Ac liyeyuyang liki mwet sulallal.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Ouinge nga kaksakin kom inmasrlon mutunfacl uh; Nga onkakin on in kaksak nu sum.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
God El sang kutangla lulap nu sin tokosra lal; El akkalemye lungse kawil lal nu sel su el sulela, Aok, nu sel David ac fita lal ma pahtpat.

< 2 Sama’ila 22 >