< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
And David spoke unto the LORD the words of this song in the day that the LORD had delivered him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul:
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
And he said, The LORD is my rock, and my fortress, and my deliverer;
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
The God of my rock; in him will I trust: he is my shield, and the horn of my salvation, my high tower, and my refuge, my saviour; you save me from violence.
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
I will call on the LORD, who is worthy to be praised: so shall I be saved from mine enemies.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
When the waves of death compassed me, the floods of ungodly men made me afraid;
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
The sorrows of hell compassed me about; the snares of death prevented me; (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
In my distress I called upon the LORD, and cried to my God: and he did hear my voice out of his temple, and my cry did enter into his ears.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
Then the earth shook and trembled; the foundations of heaven moved and shook, because he was angry.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
There went up a smoke out of his nostrils, and fire out of his mouth devoured: coals were kindled by it.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
He bowed the heavens also, and came down; and darkness was under his feet.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
And he rode upon a cherub, and did fly: and he was seen upon the wings of the wind.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
And he made darkness pavilions round about him, dark waters, and thick clouds of the skies.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Through the brightness before him were coals of fire kindled.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
The LORD thundered from heaven, and the most High uttered his voice.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
And he sent out arrows, and scattered them; lightning, and humiliated them.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
And the channels of the sea appeared, the foundations of the world were discovered, at the rebuking of the LORD, at the blast of the breath of his nostrils.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
He sent from above, he took me; he drew me out of many waters;
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
He delivered me from my strong enemy, and from them that hated me: for they were too strong for me.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
They prevented me in the day of my calamity: but the LORD was my stay.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
He brought me forth also into a large place: he delivered me, because he delighted in me.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
The LORD rewarded me according to my righteousness: according to the cleanness of my hands has he recompensed me.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
For I have kept the ways of the LORD, and have not wickedly departed from my God.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
For all his judgments were before me: and as for his statutes, I did not depart from them.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
I was also upright before him, and have kept myself from mine iniquity.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Therefore the LORD has recompensed me according to my righteousness; according to my cleanness in his eye sight.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
With the merciful you will show yourself merciful, and with the upright man you will show yourself upright.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
With the pure you will show yourself pure; and with the perverse you will show yourself unpleasing.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
And the afflicted people you will save: but your eyes are upon the haughty, that you may bring them down.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
For you are my lamp, O LORD: and the LORD will lighten my darkness.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
For by you I have run through a troop: by my God have I leaped over a wall.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
As for God, his way is perfect; the word of the LORD is tried: he is a buckler to all them that trust in him.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
For who is God, save the LORD? and who is a rock, save our God?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
God is my strength and power: and he makes my way perfect.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
He makes my feet like hinds' feet: and sets me upon my high places.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
He teaches my hands to war; so that a bow of steel is broken by mine arms.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
You have also given me the shield of your salvation: and your gentleness has made me great.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
You have enlarged my steps under me; so that my feet did not slip.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
I have pursued mine enemies, and destroyed them; and turned not again until I had consumed them.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
And I have consumed them, and wounded them, that they could not arise: yea, they are fallen under my feet.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
For you have girded me with strength to battle: them that rose up against me have you subdued under me.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
You have also given me the necks of mine enemies, that I might destroy them that hate me.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
They looked, but there was none to save; even unto the LORD, but he answered them not.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Then did I beat them as small as the dust of the earth, I did stamp them as the mire of the street, and did spread them abroad.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
You also have delivered me from the strivings of my people, you have kept me to be head of the heathen: a people which I knew not shall serve me.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Strangers shall submit themselves unto me: as soon as they hear, they shall be obedient unto me.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Strangers shall fade away, and they shall be afraid out of their close places.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
The LORD lives; and blessed be my rock; and exalted be the God of the rock of my salvation.
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
It is God that avenges me, and that brings down the people under me.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
And that brings me forth from mine enemies: you also have lifted me up on high above them that rose up against me: you have delivered me from the violent man.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Therefore I will give thanks unto you, O LORD, among the heathen, and I will sing praises unto your name.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
He is the tower of salvation for his king: and shows mercy to his anointed, unto David, and to his seed for evermore.

< 2 Sama’ila 22 >