< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
It happened after the death of Saul, that David returned from the slaughter of the Amalekites, and he stayed two days in Ziklag.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
It happened on the third day, that, look, a man came out of the camp from Saul, with his clothes torn and dirt on his head. And it came about when he came to David that he fell to the ground and paid homage.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
David said to him, "Where do you come from?" He said to him, "I have escaped out of the camp of Israel."
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
David said to him, "How did it go? Please tell me." He answered, "The people have fled from the battle, and many of the people also have fallen and are dead; and Saul and Jonathan his son are dead also."
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
David said to the young man who had told him this, "How do you know that Saul and Jonathan his son are dead?"
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
The young man who told him said, "I happened to be on Mount Gilboa and saw Saul leaning on his spear. And look, the chariots and the horsemen were closing in on him.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
When he looked behind him, he saw me, and called to me. I answered, 'Here I am.'
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
He said to me, 'Who are you?' I answered him, 'I am an Amalekite.'
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
He said to me, 'Please stand beside me, and kill me; for anguish has taken hold of me, yet there is life in me still.'
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
So I stood beside him, and killed him, because I was sure that he could not live after he had fallen. Then I took the crown that was on his head, and the bracelet that was on his arm, and have brought them here to my lord."
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Then David grabbed his clothes and tore them, and all the men with him did the same.
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
They mourned, and wept, and fasted until evening, for Saul, and for Jonathan his son, and for the people of the LORD, and for the house of Israel; because they had fallen by the sword.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
David said to the young man who had told him, "Where are you from?" He answered, "I am the son of a foreigner, an Amalekite."
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
David said to him, "How is it that you were not afraid to put forth your hand to destroy the LORD's anointed?"
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
David called one of the young men, and said, "Go near, and fall on him." He struck him, so that he died.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
David said to him, "Your blood is on your head, for your mouth has testified against you, saying, 'I have killed the LORD's anointed.'"
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
And David lamented with this lamentation over Saul and over Jonathan his son,
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
and said it should be taught to the people of Judah. Look, it is written in the book of Jashar.
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
"Your glory, Israel, is slain on your high places. How the mighty have fallen.
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Do not tell it in Gath. Do not publish it in the streets of Ashkelon, lest the daughters of the Philistines rejoice, lest the daughters of the uncircumcised celebrate.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
You mountains of Gilboa, let there be no dew nor rain on you, nor fields of offerings. For there the shield of the mighty was dishonored. The shield of Saul, no longer anointed with oil.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
From the blood of the slain, from the fat of the mighty, Jonathan's bow did not retreat. Saul's sword did not return empty.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saul and Jonathan, beloved and lovely, not separated. Lovely in their life, and in their death they were not separated. They were swifter than eagles. They were stronger than lions.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
You daughters of Israel, weep over Saul, who clothed you luxuriously in scarlet, who put ornaments of gold on your clothing.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
How are the mighty fallen in the midst of the battle. Jonathan is slain on your high places.
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
I grieve for you, my brother Jonathan. You have been very pleasant to me. Your love for me was a wonder, more than the love of women.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
How are the mighty fallen, and the weapons of war perished."

< 2 Sama’ila 1 >