< 2 Sarakuna 6 >

1 Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
Sinovi prerokov so Elizeju rekli: »Glej torej, kraj, kjer prebivamo s teboj, je za nas preveč utesnjen.
2 Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
Naj gremo, prosimo te, k Jordanu in si od tam vsak mož vzame bruno in si tam zgradimo kraj, kjer bomo lahko prebivali.« Odgovoril je: »Pojdite.«
3 Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
Nekdo je rekel: »Bodi zadovoljen, prosim te in pojdi s svojimi služabniki.« Odgovoril je: »Šel bom.«
4 Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
Tako je šel z njimi. In ko so prišli k Jordanu, so sekali les.
5 Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
Toda ko je nekdo podiral drevo, je glava sekire padla v vodo in zavpil je ter rekel: »Ojoj, gospod! Kajti bila je izposojena.«
6 Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
Božji mož je rekel: »Kam je padla?« Ta mu je pokazal kraj. In odsekal je palico ter jo vrgel tja in železo je zaplavalo.
7 Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
Zato je rekel: »Vzemi to k sebi.« In iztegnil je svojo roko in jo vzel.
8 To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
Potem se je sirski kralj vojskoval zoper Izraela in se posvetoval s svojimi služabniki, rekoč: »Na tem in tem kraju bo moj tabor.«
9 Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
Božji mož pa je k Izraelovemu kralju poslal, rekoč: »Pazi, da ne greš mimo tega kraja, kajti tja dol so prišli Sirci.«
10 Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
Izraelov kralj je poslal h kraju, o katerem mu je povedal Božji mož, ga o njem posvaril in tam se je rešil, ne samo enkrat ali dvakrat.
11 Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
Zato je bilo srce sirskega kralja zaradi te stvari boleče vznemirjeno. Poklical je svoje služabnike in jim rekel: »Ali mi ne boste pokazali, kdo izmed nas je za Izraelovega kralja?«
12 Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
Nekdo izmed njegovih služabnikov je rekel: »Nihče, moj gospod, oh kralj, temveč prerok Elizej, ki je v Izraelu, govori Izraelovemu kralju besede, ki jih ti govoriš v svoji spalnici.«
13 Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
Rekel je: »Pojdi in poglej, kje je, da bom lahko poslal in ga zgrabil.« Bilo mu je povedano, rekoč: »Glej, on je v Dotánu.«
14 Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
Zato je tja poslal konje, bojne vozove in veliko vojsko. Prišli so ponoči in obkolili mesto.
15 Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
Ko je služabnik Božjega moža zgodaj vstal in odšel naprej, glej, vojska je obkolila mesto, tako s konji kakor bojnimi vozovi. Njegov služabnik mu je rekel: »Ojoj, moj gospod! Kaj bomo storili?«
16 Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
Odgovoril je: »Ne boj se, kajti tistih, ki so z nami, je več kakor tistih, ki so z njimi.«
17 Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
Elizej je molil in rekel: » Gospod, prosim te, odpri njegove oči, da bo lahko videl.« Gospod je odprl oči mladeniča in ta je videl in glej, gora je bila polna konj in ognjenih bojnih voz naokoli Elizeja.
18 Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
Ko so prišli dol k njemu, je Elizej molil h Gospodu in rekel: »Udari to ljudstvo, prosim te, s slepoto.« In udaril jih je s slepoto glede na Elizejevo besedo.
19 Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
Elizej jim je rekel: »To ni pot niti ni to mesto. Sledite mi in privedel vas bom k človeku, ki ga iščete.« Toda odvedel jih je v Samarijo.
20 Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
Ko so prišli v Samarijo, se je pripetilo, da je Elizej rekel: » Gospod, odpri oči teh mož, da bodo lahko videli.« In Gospod je odprl njihove oči in so videli in glej, bili so sredi Samarije.
21 Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
Ko jih je Izraelov kralj videl, je rekel Elizeju: »Moj oče, ali naj jih udarim? Ali naj jih udarim?«
22 Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
Ta pa je odgovoril: »Ne boš jih udaril. Mar bi udaril tiste, ki si jih odvedel ujete s svojim mečem in s svojim lokom? Prednje postavi kruh in vodo, da bodo lahko jedli in pili in šli k svojemu gospodarju.«
23 Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
Zanje je pripravil veliko preskrbo in ko so pojedli in popili, jih je poslal proč in odšli so k svojemu gospodarju. Tako čete iz Sirije niso nič več prihajale v deželo Izrael.
24 Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
Po tem se je pripetilo, da je sirski kralj Ben Hadád zbral vso svojo vojsko, odšel gor in oblegal Samarijo.
25 Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
Tam v Samariji pa je bila velika lakota. Glej, oblegali so jo, dokler ni bila oslovska glava prodana za osemdeset koščkov srebra in četrtinka kaba golobjega iztrebka za pet koščkov srebra.
26 Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
Medtem ko se je Izraelov kralj sprehajal po obzidju, je k njemu zavpila ženska, rekoč: »Pomagaj, moj gospod, oh kralj.«
27 Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
Ta ji je rekel: »Če ti Gospod ne pomaga, od kod naj ti jaz pomagam? Iz skednja ali iz vinske stiskalnice?«
28 Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
Kralj ji je rekel: »Kaj te pesti?« Odgovorila je: »Ta ženska mi je rekla: ›Daj svojega sina, da ga bomo lahko danes pojedli, mojega sina pa bomo pojedli jutri.‹«
29 Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
Tako smo skuhali mojega sina in ga pojedli. Naslednji dan pa sem ji rekla: »Daj svojega sina, da ga bomo lahko pojedli.« Ona pa je svojega sina skrila.
30 Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
Pripetilo se je, ko je kralj slišal besede ženske, da je pretrgal svoja oblačila. Prek obzidja je šel mimo in ljudstvo je gledalo in glej, na svojem telesu je imel spodaj vrečevino.
31 Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
Potem je rekel: »Bog naj mi stori tako in še več, če bo glava Šafátovega sina Elizeja, ta dan obstala na njem.«
32 To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
Toda Elizej je sedel v svoji hiši in starešine so sedeli z njim. In kralj je izpred sebe poslal moža, toda malo preden je poslanec prišel k njemu, je starešinam rekel: »Ali vidite, kako je ta sin morilca poslal, da mi vzame mojo glavo? Poglejte, ko pride poslanec, zaprite vrata in ga trdno držite pri vratih. Mar ni zvok stopal njegovega gospodarja za njim?«
33 Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”
Medtem ko je še govoril z njimi, glej, je dol k njemu prišel poslanec in rekel: »Glej to zlo je od Gospoda. Zakaj bi še čakal na Gospoda?«

< 2 Sarakuna 6 >