< 2 Sarakuna 1 >

1 Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
Moab rebelled against Israel after the death of Ahab.
2 Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
Then Ahaziah fell down through the lattice in his upper chamber in Samaria, and was injured. So he sent for messengers and said to them, “Go, ask Baal-Zebub, the god of Ekron, whether I will recover from this injury.”
3 Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
But the angel of Yahweh said to Elijah the Tishbite, “Arise, go up to meet the messengers of the king of Samaria, and ask them, 'Is it because there is no God in Israel that you are going to consult with Baal-Zebub, the god of Ekron?
4 Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
Therefore Yahweh says, “You will not come down from the bed to where you have gone up; instead, you will certainly die.”'” Then Elijah left.
5 Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
When the messengers returned to Ahaziah, he said to them, “Why have you returned?”
6 Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
They said to him, “A man came to meet us who said to us, 'Go back to the king who sent you, and say to him, “Yahweh says this: 'Is it because there is no God in Israel that you sent men to consult with Baal-Zebub, the god of Ekron? Therefore you will not come down from the bed to which you have gone up; instead, you will certainly die.'”'”
7 Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
Ahaziah said to his messengers, “What sort of man was he, the one who came up to meet you and said these words to you?”
8 Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
They answered him, “He wore a garment made of hair and had a leather belt wrapped around his waist.” So the king replied, “That is Elijah the Tishbite.”
9 Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
Then the king sent a captain with fifty soldiers to Elijah. The captain went up to Elijah where he was sitting on the top of a hill. The captain spoke to him, “You, man of God, the king has said, 'Come down.'”
10 Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
Elijah answered and said to the captain, “If I am a man of God, let fire come down from heaven and consume you and your fifty men.” Then fire came down from heaven and consumed him and his fifty men.
11 Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
Again King Ahaziah sent to Elijah another captain with fifty soldiers. This captain also said to Elijah, “You, man of God, the king says, 'Come down quickly.'”
12 Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
Elijah answered and said to them, “If I am a man of God, let fire come down from heaven and consume you and your fifty men.” Again the fire of God came down from heaven and consumed him and his fifty men.
13 Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
Yet again the king sent a third group of fifty warriors. This captain went up, fell on his knees before Elijah, and implored him and said to him, “You, man of God, I ask you, let my life and the life of these fifty servants of yours be precious in your sight.
14 Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
Indeed, fire came down from heaven and consumed the first two captains with their men, but now let my life be precious in your sight.”
15 Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
The angel of Yahweh said to Elijah, “Go down with him. Do not be afraid of him.” So Elijah arose and went down with him to the king.
16 Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
Later Elijah said to Ahaziah, “This is what Yahweh says, 'You have sent messengers to consult with Baal-Zebub, the god of Ekron. Is it because there is no God in Israel from whom you can ask for information? So now, you will not come down from the bed where you have gone up; you will certainly die.'”
17 Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
So King Ahaziah died according to the word of Yahweh that Elijah had spoken. Joram began to reign in his place, in the second year of Jehoram son of Jehoshaphat king of Judah, because Ahaziah had no son.
18 Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?
As for the other matters concerning Ahaziah, are they not written in the book of the events of the kings of Israel?

< 2 Sarakuna 1 >