< 2 Korintiyawa 6 >

1 A matsayinmu na abokan aikin Allah, muna roƙonku kada ku karɓi alherin Allah a banza.
And working together also we call upon [you] that ye receive not in vain the grace of God —
2 Gama ya ce, “A lokacin samun alherina, na ji ka, a ranar samun ceto kuma, na taimake ka.” Ina gaya muku, yanzu ne lokacin samun alherin Allah, yanzu ne ranar samun ceto.
for He saith, 'In an acceptable time I did hear thee, and in a day of salvation I did help thee, lo, now [is] a well-accepted time; lo, now, a day of salvation,' —
3 Ba ma sa abin tuntuɓe wa kowa, domin kada hidimarmu ta zama abin zargi.
in nothing giving any cause of offence, that the ministration may be not blamed,
4 A maimakon haka, duk abin da muke yi, muna yin shi ne don mu nuna cewa mu masu hidimar Allah ne. Muna yin haka cikin jimrewa, da shan wahala, da shan wuya, har da shan masifu.
but in everything recommending ourselves as God's ministrants; in much patience, in tribulations, in necessities, in distresses,
5 Da shan dūka, da shan dauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rashin barci, da kuma yunwa.
in stripes, in imprisonments, in insurrections, in labours, in watchings, in fastings,
6 Da cikin tsarki, da fahimta, da haƙuri, da kirki, da cikin Ruhu Mai Tsarki, da cikin ƙauna mai gaskiya,
in pureness, in knowledge, in long-suffering, in kindness, in the Holy Spirit, in love unfeigned,
7 da cikin magana mai gaskiya, da kuma cikin ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu,
in the word of truth, in the power of God, through the armour of the righteousness, on the right and on the left,
8 ta wurin ɗaukaka da ƙasƙanci, da cikin ɓata suna, da kuma cikin yabo. Cikin faɗin gaskiya, an ɗauke mu masu ƙarya,
through glory and dishonour, through evil report and good report, as leading astray, and true;
9 mu sanannu ne, duk da haka an ɗauke mu kamar ba a san mu ba, muna mutuwa, duk da haka a raye muke, an ba mu horo, duk da haka ba a kashe mu ba,
as unknown, and recognized; as dying, and lo, we live; as chastened, and not put to death;
10 cikin baƙin ciki, duk da haka kullum cikin murna muke. Cikin matalauta, duk da haka muna azurtar da mutane da yawa. Ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne.
as sorrowful, and always rejoicing; as poor, and making many rich; as having nothing, and possessing all things.
11 Ya ku Korintiyawa, mun yi muku magana a sake, muka kuma saki zuciya da ku ƙwarai.
Our mouth hath been open unto you, O Corinthians, our heart hath been enlarged!
12 Ba mu ƙi nuna muku ƙaunarmu ba, sai dai ku kuka ƙi nuna mana.
ye are not straitened in us, and ye are straitened in your [own] bowels,
13 A wannan zance kam, ina magana da ku kamar’ya’yana, ku ma ku saki zuciya da mu.
and [as] a recompense of the same kind, (as to children I say [it], ) be ye enlarged — also ye!
14 Kada ku haɗa kai da marasa bi. Gama me ya haɗa adalci da mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu?
Become not yoked with others — unbelievers, for what partaking [is there] to righteousness and lawlessness?
15 Wace daidaituwa ce tsakanin Kiristi da Iblis? Me ya haɗa mai bi da marar bi?
and what fellowship to light with darkness? and what concord to Christ with Belial? or what part to a believer with an unbeliever?
16 Wane alkawari ne tsakanin haikalin Allah da na gumaka? Gama mu haikalin Allah mai rai ne. Kamar yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi tafiya a cikinsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
and what agreement to the sanctuary of God with idols? for ye are a sanctuary of the living God, according as God said — 'I will dwell in them, and will walk among [them], and I will be their God, and they shall be My people,
17 Saboda haka, “Sai ku fito daga cikinsu, ku keɓe kanku, in ji Ubangiji. Kada ku taɓa wani abu marar tsabta, zan kuma karɓe ku.”
wherefore, come ye forth out of the midst of them, and be separated, saith the Lord, and an unclean thing do not touch, and I — I will receive you,
18 Kuma, “Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama’ya’yana, maza da mata, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
and I will be to you for a Father, and ye — ye shall be to Me for sons and daughters, saith the Lord Almighty.'

< 2 Korintiyawa 6 >