< 2 Korintiyawa 5 >

1 Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. (aiōnios g166)
For we know that if our earthly house of this tabernacle were dissolved, we have a building of God, an house not made with hands, eternal in the heavens. (aiōnios g166)
2 Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama,
For in this we groan, earnestly desiring to be clothed on with our house which is from heaven:
3 don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba.
If so be that being clothed we shall not be found naked.
4 Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa.
For we that are in this tabernacle do groan, being burdened: not for that we would be unclothed, but clothed on, that mortality might be swallowed up of life.
5 Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.
Now he that has worked us for the selfsame thing is God, who also has given to us the earnest of the Spirit.
6 Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji.
Therefore we are always confident, knowing that, whilst we are at home in the body, we are absent from the Lord:
7 Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba.
(For we walk by faith, not by sight: )
8 Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji.
We are confident, I say, and willing rather to be absent from the body, and to be present with the Lord.
9 Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan.
Why we labor, that, whether present or absent, we may be accepted of him.
10 Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.
For we must all appear before the judgment seat of Christ; that every one may receive the things done in his body, according to that he has done, whether it be good or bad.
11 To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku.
Knowing therefore the terror of the Lord, we persuade men; but we are made manifest to God; and I trust also are made manifest in your consciences.
12 Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya.
For we commend not ourselves again to you, but give you occasion to glory on our behalf, that you may have somewhat to answer them which glory in appearance, and not in heart.
13 In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne.
For whether we be beside ourselves, it is to God: or whether we be sober, it is for your cause.
14 Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu.
For the love of Christ constrains us; because we thus judge, that if one died for all, then were all dead:
15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.
And that he died for all, that they which live should not from now on live to themselves, but to him which died for them, and rose again.
16 Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka.
Why from now on know we no man after the flesh: yes, though we have known Christ after the flesh, yet now from now on know we him no more.
17 Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo!
Therefore if any man be in Christ, he is a new creature: old things are passed away; behold, all things are become new.
18 Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu,
And all things are of God, who has reconciled us to himself by Jesus Christ, and has given to us the ministry of reconciliation;
19 wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu.
To wit, that God was in Christ, reconciling the world to himself, not imputing their trespasses to them; and has committed to us the word of reconciliation.
20 Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah.
Now then we are ambassadors for Christ, as though God did beseech you by us: we pray you in Christ’s stead, be you reconciled to God.
21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.
For he has made him to be sin for us, who knew no sin; that we might be made the righteousness of God in him.

< 2 Korintiyawa 5 >