< 2 Tarihi 9 >

1 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ji shahararr Solomon, sai ta zo Urushalima tă gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta iso tare da ayari mai girma, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja, ta zo wurin Solomon ta kuma yi magana da shi game da dukan abin da yake zuciyarta.
When the queen of Sheba heard of Solomon's fame, she came to Jerusalem to test him with hard questions. She came with a very long caravan, with camels loaded with spices, much gold, and many precious gemstones. When she had come to Solomon, she told him all that was in her heart.
2 Solomon ya amsa dukan tambayoyinta; babu wani abin da ya yi masa wuya yă bayyana mata.
Solomon answered her all her questions; nothing was too difficult for Solomon; there was no question that he did not answer.
3 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Solomon da kuma fadan da ya gina,
When the queen of Sheba saw Solomon's wisdom and the palace that he had built,
4 ta ga abincin da yake teburinsa, ta ga zaman fadawansa, bayi masu yin masa hidima cikin rigunansu, ta ga masu riƙe kwaf cikin rigunansu da kuma hadayun ƙonawar da ya yi a haikalin Ubangiji, sai mamaki ya kama ta.
the food on his table, the seating of his servants, the work of his servants and their clothing, also his cupbearers and their clothing, and the burnt offerings he made at the house of Yahweh, and there was no more breath in her.
5 Ta ce wa sarki, “Labarin da na ji a ƙasata game da nasarorinka da hikimarka, gaskiya ne.
She said to the king, “It is true, the report that I heard in my own land of your words and your wisdom.
6 Amma ban gaskata abin da suka faɗa ba sai da na zo na kuma gani da idanuna. Tabbatacce, ko rabin girman hikimarka ba a faɗa mini ba, ka wuce labarin da na ji nesa ba kusa ba.
I did not believe what I heard until I came here, and now my eyes have seen it. Not half was told me about your wisdom and wealth! You have exceeded the fame that I heard about.
7 Abin farin ciki ne ga mutanenka! Abin farin ciki ne ga fadawanka, waɗanda suke cin gaba da tsayawa a gabanka suna kuma jin hikimarka!
How blessed are your people, and how blessed are your servants who constantly stand before you, because they hear your wisdom.
8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka, wanda ya ji daɗi a cikinka ya sa ka a kan kujerar sarautarsa a matsayin sarki don ka yi mulkin domin Ubangiji Allahnka. Saboda ƙaunar Allahnka wa Isra’ila da kuma sha’awarsa na riƙe su har abada, ya naɗa ka sarki a bisansu, don ka yi adalci da kuma gaskiya.”
Blessed be Yahweh your God, who has taken pleasure in you, who placed you on his throne, to be king for Yahweh your God. Because your God loved Israel, in order to establish them forever, he had made you king over them, for you to do justice and righteousness!”
9 Sa’an nan ta ba sarki talenti 120 na zinariya, kayan yaji masu yawa, da kuma duwatsu masu daraja. Ba a taɓa kasance da irin kayan yaji mai yawa kamar waɗanda sarauniyar Sheba ta ba wa sarki Solomon ba.
She gave the king 120 talents of gold and a large amount of spices and precious stones. No greater amount of spices as these that the queen of Sheba gave to King Solomon was ever given to him again.
10 (Mutanen Hiram da mutanen Solomon suka kawo zinariya daga Ofir, suka kuma kawo gungumen algum da duwatsu masu daraja.
The servants of Hiram and the servants of Solomon, who brought gold from Ophir, also brought algum wood and precious stones.
11 Sarki ya yi amfani da gungumen algum don matakalan haikalin Ubangiji da kuma na fadan sarki, ya kuma yi garayu da molaye don mawaƙa. Ba a taɓa gani irinsu a Yahuda ba.)
With the algum wood, the king made steps for the house of Yahweh and for his house, as well as harps and lyres for the musicians. No wood like this had been seen before in the land of Judah.
12 Sarki Solomon ya ba sarauniyar Sheba duk abin da take so da kuma ta nema; ya ba ta fiye da abin da ta kawo masa. Sa’an nan ta tashi ta koma ƙasarta tare da masu rufe mata baya.
King Solomon gave to the queen of Sheba everything she desired and whatever she asked for; he gave her more than what she had brought to the king. So she left and went back to her own land, she and her servants.
13 Nauyin zinariyar da Solomon yake karɓa shekara-shekara talenti 666 ne,
Now the weight of gold that came to Solomon in one year was 666 talents of gold,
14 ban da harajin da fatakai da’yan kasuwa suke biya. Haka kuma dukan sarakunan Arabiya da gwamnonin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa wa Solomon.
besides the gold that the traders and merchants brought. All the kings of Arabia and the governors in the country also brought gold and silver to Solomon.
15 Sarki Solomon ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu da zinariya; an yi kowane garkuwa da bekas ɗari shida na zinariya.
King Solomon made two hundred large shields of beaten gold. Six hundred shekels of gold went into each one.
16 Ya kuma yi ƙanana garkuwoyi zinariya ɗari uku, da bekas ɗari uku na zinariya a kowanne. Sarki ya sa su a cikin Fadan da ake kira Kurmin Lebanon.
He also made three hundred shields of beaten gold. Three minas of gold went into each shield; the king put them into the House of the Forest of Lebanon.
17 Sai sarki ya yi wata kujerar sarauta mai girma da aka shafe ta da hauren giwa, aka kuma dalaye ta da zinariya zalla.
Then the king made a great throne of ivory and overlaid it with the finest gold.
18 Kujerar tana da matakalai shida, da wurin sa ƙafa na zinariya haɗe da ita. A kowane gefen wurin zama, akwai wurin ajiye hannu, da zaki tsaye kusa da kowannensu.
There were six steps to the throne, and a footstool was attached to the throne. On each side of the throne there were armrests with two lions standing beside each of them.
19 Zakoki goma sha biyu sun tsaya a kan matakalai shida, ɗaya a ƙarshen matakala guda. Ba a taɓa yin irin wannan abu don wata masarauta ba.
Twelve lions stood on the steps, one on each side of each of the six steps. There was no throne like it in any other kingdom.
20 Dukan kwaf na Sarki Solomon zinariya ne, kuma dukan kayayyakin gida a Fadan da ake kira Kurmin Lebanon zinariya ne zalla. Ba a yi wani abu da azurfa ba, domin ba a ɗauki azurfa a zamanin Solomon a bakin kome ba.
All King Solomon's drinking cups were gold, and all the drinking cups in the House of the Forest of Lebanon were of pure gold. None were silver because silver was not considered valuable in Solomon's days.
21 Sarki yana da jerin jiragen ruwa na kasuwanci waɗanda mutanen Hiram ne suke kula da su. Sau ɗaya kowace shekara uku sukan dawo ɗauke da zinariya, azurfa, hauren giwa, gogo da kuma birai.
The king had at sea a fleet of oceangoing ships, along with the fleet of Hiram. Once every three years the fleet brought gold, silver, and ivory, as well as apes and baboons.
22 Sarki Solomon ya fi arziki da hikima in aka kwatanta da dukan sauran sarakunan duniya.
So King Solomon exceeded all the kings of the world in riches and in wisdom.
23 Dukan sarakunan duniya sun nemi su sadu da Solomon don su ji hikimar da Allah ya sa a zuciyarsa.
All the kings of the earth sought the presence of Solomon in order to hear his wisdom, which God had put in his heart.
24 Shekara, shekara, duk wanda ya zo wurinsa yakan kawo kyauta, kayayyakin azurfa da na zinariya, da riguna, makamai da kayan yaji, da dawakai da kuma alfadarai.
Those who visited brought tribute, vessels of silver and of gold, clothes, armor, and spices, as well as horses and mules, year after year.
25 Solomon ya kasance da wuraren ajiye dawakai dubu huɗu don dawakai da kekunan yaƙi, yana da dawakai dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi da kuma tare da shi a Urushalima.
Solomon had four thousand stalls for horses and chariots, and twelve thousand horsemen, which he stationed in the chariot cities and with himself in Jerusalem.
26 Ya yi mulki bisa dukan sarakuna daga Kogi Yuferites zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar.
He ruled over all the kings from the Euphrates River to the land of the Philistines, and to the border of Egypt.
27 Sarki ya sa azurfa ta zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma da yawa kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
The king had silver in Jerusalem, as much as the stones on the ground. He made cedar wood to be as abundant as the sycamore fig trees that are in the lowlands.
28 An sayo dawakan Solomon daga Masar da kuma daga dukan sauran ƙasashe.
They brought horses for Solomon from Egypt and from all the lands.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin annabi Natan, cikin annabcin Ahiya mutumin Shilo da kuma cikin wahayin Iddo mai gani game da Yerobowam ɗan Nebat.
As for the other matters concerning Solomon, first and last, are they not written in The History of Nathan the Prophet, in The Prophecy of Ahijah the Shilonite, and in The Visions of Iddo the Seer (which also had information about Jeroboam son of Nebat)?
30 Solomon ya yi mulki a Urushalima a bisa dukan Isra’ila shekaru arba’in.
Solomon reigned in Jerusalem over all Israel for forty years.
31 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi cikin birnin Dawuda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
He slept with his ancestors and the people buried him in the city of David his father. Rehoboam, his son, became king in his place.

< 2 Tarihi 9 >