< 2 Tarihi 7 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Da Salomo havde endt sin Bøn, for Ild ned fra Himmelen og fortærede Brændofferet og Slagtofrene, og HERRENs Herlighed fyldte Templet,
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
og Præsterne kunde ikke gå ind i HERRENs Hus, fordi HERRENs Herlighed fyldte det.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Og da alle Israeliterne så Ilden og HERRENs Herlighed fare ned over Templet, kastede de sig på Knæ på Stenbroen med Ansigtet mod Jorden og filbad og lovede HERREN med Ordene "thi han er god, og hans Miskundhed varer evindelig!"
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Kongen ofrede nu sammen med alt Folket Slagtofre for HEERRENs Åsyn.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
Til Slagtofferet tog Kong Salomo 22.000 Stykker Hornkvæg og 120.000 Stykker Småkvæg. Således indviede Kongen og alt Folket Guds Hus.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Og Præsterne stod på deres Pladser, og Leviterne stød med HERRENs Musikinstrumenter, som Kong David havde ladet lave, for at love HERREN med Davids Lovsangs Ord "thi hans Miskundhed varer evindelig!" og Præsterne stod lige over for dem og blæste i trompeter, og hele Israel stod op:
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Og Salomo helligede den mellemste Del af Forgården foran HERRENs Hus, thi der måtte han ofre Brændofrene og Fedtstykkerne af Takofrene, da Kobberalteret, som Salomo havde ladet lave, ikke kunde rumme Brændofferet, Afgrødeoffret og Fedtstykkerne.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
Samtidig fejrede Salomo i syv Dage Højtiden sammen med hele Israel, en vældig Forsamling lige fra Egnen ved Hamat og til Ægyptens Bæk.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Ottendedagen holdt man festlig Samling, thi de fejrede Alterets Indvielse i syv Dage og Højtiden i syv.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
Og på den tre og tyvende Dag i den syvende Måned lod han Folket gå hver til sit, glade og vel til Mode over den Godhed, HERREN havde vist sin Tjenet David og Salomo og sit Folk Israel.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Salomo var nu færdig med at opføre HERRENs Hus og Kongens Palads; og alt, hvad Salomo havde sat sig for at udføre ved HERRENs Hus og sit Palads, havde han lykkeligt ført igennem.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Da lod HERREN sig til Syne for Salomo om Natten og sagde til ham: "Jeg har hørt din Bøn og udvalgt mig dette Sted til Offersted.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Dersom jeg tillukker Himmelen, så Regnen udebliver, eller jeg opbyder Græshopperne til at æde Landet op, eller jeg sender Pest i mit Folk,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
og mit Folk, som mit Navn nævnes over, da ydmyger sig, beder og søger mit Åsyn og vender om fra deres onde Veje, så vil jeg høre det i Himmelen og tilgive deres Synd og læge deres Land,
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Nu skal mine Øjne være åbne og mine Ører lytte til Bønnen, der bedes på dette Sted.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
Og nu har jeg udvalgt og billiget dette Hus, for at mit Navn kan bo der til evig Tid, og mine Øjne og mit Hjerte skal være der alle Dage.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Hvis du nu vandrer for mit Åsyn som din Fader David, så du gør alt, hvad. jeg har pålagt dig, og, holder mine Anordninger og Lovbud,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
så vil jeg opretholde din Kongetrone, som jeg tilsagde din Fader David, da jeg sagde: En Efterfølger skal aldrig fattes dig til at herske over Israel.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Men hvis I vender eder bort og forlader mine Anordninger og Bud, som jeg har forelagt eder, og går hen og dyrker fremmede Guder og tilbeder dem,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
så vil jeg rykke eder op fra mit Land, som jeg gav eder; og dette Hus, som jeg har belliget for mit Navn, vil jeg forkaste fra mit Åsyn og gøre det til Spot og Spe blandt alle Folk,
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
og dette Hus, som var så ophøjet, over det skal enhver, som kommer der forbi, blive slået af Rædsel. Og når man siger: Hvorfor har HERREN handlet således mod dette Land og dette Hus?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
skal der svares: Fordi de forlod HERREN, deres Fædres Gud, som førte dem ud af Ægypten, og holdt sig til andre Guder, tilbad og dyrkede dem; derfor har HERREN bragt al denne Elendighed over dem!"

< 2 Tarihi 7 >