< 2 Tarihi 32 >

1 Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
Après ces choses et ces actes de fidélité, Sennachérib, roi d'Asssyrie, se mit en marche et, étant entré en Juda, il campa contre les villes fortes, dans le dessein de s'en emparer.
2 Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
Quand Ezéchias vit que Sennachérib était venu et qu'il se tournait contre Jérusalem pour l'attaquer,
3 sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
il tint conseil avec ses chefs et ses hommes vaillants, afin de couvrir les eaux des sources qui étaient hors de la ville, et ils lui prêtèrent secours.
4 Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
Un peuple nombreux se rassembla, et ils couvrirent tontes les sources et le ruisseau qui coulait au milieu du pays, en disant: " Pourquoi les rois d'Assyrie, en venant ici, trouveraient-ils des eaux abondantes? "
5 Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
Ezéchias prit courage; il rebâtit toute la muraille qui était en ruine et restaura les tours; il bâtit l'autre mur en dehors, fortifia Mello dans la cité de David; il fit fabriquer une quantité d'armes et de boucliers.
6 Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
Il donna des chefs militaires au peuple et, les ayant réunis prés de lui sur la place de la porte de la ville, il leur parla au cœur, en disant:
7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
" Soyez forts et courageux; ne craignez point et ne vous effrayez point devant le roi d'Assyrie et devant toute la multitude qui est avec lui; car il y a plus avec nous qu'avec lui.
8 Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
Avec lui est un bras de chair, et avec nous est Yahweh, notre Dieu, pour nous aider et mener nos combats. " Le peuple eut confiance dans les paroles d'Ezéchias, roi de Juda.
9 Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
Après cela, Sennachérib, roi d'Assyrie, envoya ses serviteurs a Jérusalem, — il était devant Lachis avec toutes ses forces royales, — vers Ezéchias, roi de Juda, et vers tous ceux de Juda qui étaient à Jérusalem, pour leur dire:
10 “Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
" Ainsi dit Sennachérib, roi d'Assyrie: En quoi vous confiez-vous, pour que vous restiez assiégés à Jérusalem dans la détresse?
11 Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
Ezéchias ne vous trompe-t-il pas pour vous livrer à la mort par la famine et par la soif, quand il dit: Yahweh notre Dieu nous sauvera de la main du roi d'Assyrie?
12 Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
N'est-ce pas lui, Ezéchias, qui a fait disparaître les hauts lieux et les autels de Yahweh, en disant à Juda et à Jérusalem: Vous vous prosternerez devant un seul autel, et vous y offrirez des parfums?
13 “Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
Ne savez-vous pas ce que nous avons fait, mes pères et moi, à tous les peuples des pays? Les dieux des peuples des pays ont-ils pu vraiment sauver leur pays de ma main?
14 Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
Quel est, parmi tous les dieux de ces nations que mes pères ont exterminées, celui qui a pu délivrer son peuple de ma main, pour que votre dieu puisse vous délivrer de ma main?
15 Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
Et maintenant, qu'Ezéchias ne vous séduise point et ne vous trompe pas ainsi! Ne vous fiez pas à lui. Car aucun dieu d'aucune nation ni d'aucun royaume n'a pu délivrer son peuple de ma main et de la main de mes pères: combien moins votre dieu vous délivrera-t-il de ma main! "
16 Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
Les serviteurs de Sennachérib parlèrent encore contre Yahweh Dieu et contre Ezéchias, son serviteur.
17 Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
Il écrivit aussi une lettre pour insulter Yahweh, le Dieu d'Israël, et pour parler contre lui; il s'exprimait en ces termes: " De même que les dieux des nations des pays n'ont pu délivrer leur peuple de ma main, de même le dieu d'Ezéchias ne délivrera pas son peuple de ma main. "
18 Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
Et ses serviteurs crièrent à haute voix, en langue judaïque, au peuple de Jérusalem qui était sur la muraille, pour l'effrayer et l'épouvanter, afin de pouvoir ainsi s'emparer de la ville.
19 Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
Ils parlaient du Dieu de Jérusalem comme des dieux des peuples de la terre, ouvrages de mains d'homme.
20 Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
A cause de cela, le roi Ezéchias et le prophète Isaïe, fils d'Amos, se mirent à prier, et ils crièrent vers le ciel.
21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
Et Yahweh envoya un ange qui extermina tous les vaillants hommes, les princes et les chefs dans le camp du roi d'Assyrie. Le roi s'en retourna couvert de honte dans son pays. Lorsqu'il fut entré dans la maison de son dieu, quelques-uns de ceux qui étaient sortis de ses entrailles le firent tomber par l'épée.
22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
Et Yahweh sauva Ezéchias et les habitants de Jérusalem de la main de Sennachérib, roi d'Assyrie, et de la main de tous ses ennemis, et il les guida de tous côtés.
23 Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
Beaucoup de gens apportèrent à Jérusalem des offrandes à Yahweh, et de riches présents à Ezéchias, roi de Juda, qui fut élevé depuis lors aux yeux de toutes les nations.
24 A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
En ce temps-là, Ezéchias fut malade à la mort. Il pria Yahweh, et Yahweh lui parla et lui accorda un prodige.
25 Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
Mais Ezéchias ne répondît pas au bienfait qu'il avait reçu, car son cœur s'éleva, et la colère de Yahweh fut sur lui, ainsi que sur Juda et Jérusalem.
26 Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
Et Ezéchias s'humilia à cause de l'orgueil de son cœur, lui et les habitants de Jérusalem, et la colère de Yahweh ne vint pas sur eux pendant la vie d'Ezéchias.
27 Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
Ezéchias eut beaucoup de richesses et de gloire. Il amassa des trésors d'argent, d'or, de pierres précieuses, d'aromates, de boucliers et de toutes sortes d'objets désirables.
28 Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
Il se fit des magasins pour les produits en blé, en vin et en huile, des crèches pour toute espèce de bétail, et il eut des troupeaux pour les étables.
29 Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
Il se bâtit des villes, et il eut de nombreux troupeaux de bœufs et de brebis, car Dieu lui donna des biens considérables.
30 Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
Ce fut lui aussi, Ezéchias, qui couvrit l'issue supérieure des eaux du Gihon, et les dirigea en bas vers l'occident de la cité de David. Ezéchias réussit dans toutes ses entreprises.
31 Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
Et Dieu ne l'abandonna aux messagers que les chefs de Babylone envoyèrent auprès de lui pour s'informer du prodige qui avait eu lieu dans le pays, que pour l'éprouver, afin de connaître tout ce qu'il y avait dans son cœur.
32 Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Le reste des actes d'Ezéchias, et ses œuvres pieuses, voici que cela est écrit dans la Vision du prophète Isaïe, fils d'Amos, et dans le livre des rois de Juda et d'Israël.
33 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Ezéchias se coucha avec ses pères, et on l'enterra dans le lieu le plus élevé des sépulcres des fils de David; et tout Juda et les habitants de Jérusalem lui rendirent des honneurs à sa mort. Et Manassé, son fils, régna à sa place.

< 2 Tarihi 32 >