< 2 Tarihi 27 >

1 Yotam yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
Jotham avait vingt-cinq ans à son avènement et il régna seize ans à Jérusalem. Or le nom de sa mère était Jerusa, fille de Tsadoc.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda mahaifinsa Uzziya ya yi, sai dai bai kutsa cikin haikalin Ubangiji kamar mahaifinsa ba. Mutane kuwa, suka ci gaba da aikata ayyukan lalaci.
Et il fit ce qui est bien aux yeux de l'Éternel, en tout à l'exemple de Hozias, son père, seulement il ne s'introduisit pas dans le Temple de l'Éternel; le peuple se corrompait encore.
3 Yotam ya sāke ginin Ƙofar Bisa na haikalin Ubangiji, ya kuma yi aiki sosai a katanga a tudun Ofel.
Et il construisit la porte supérieure du Temple de l'Éternel, et il fit beaucoup de travaux aux murs d'Ophel.
4 Ya gina garuruwa a tuddan Yahuda, ya giggina katanga da gine-gine masu tsawo a wuraren da suke a kurmi.
Et il bâtit des villes dans la montagne de Juda, et dans les forêts il bâtit des châteaux et des tours.
5 Yotam ya yi yaƙi da sarkin Ammonawa ya kuma ci su. A wannan shekara Ammonawa suka biya shi haraji talenti ɗari na azurfa, garwan alkama dubu goma da kuma garwa dubu goma na sha’ir. Ammonawa suka kawo masa wannan kuma a shekara ta biyu da ta uku.
Et il eut guerre avec le roi des Ammonites, et il les vainquit, et les Ammonites lui payèrent cette année-là cent talents d'argent et dix mille cors de froment et dix mille d'orge. C'est ce que lui payèrent les Ammonites aussi la seconde année et la troisième.
6 Yotam ya ƙaru a iko saboda ya daidaita al’amuransa a gaban Ubangiji Allahnsa.
Et Jotham devint puissant, parce qu'il réglait ses voies devant l'Éternel son Dieu.
7 Sauran ayyuka a mulkin Yotam, haɗe da dukan yaƙe-yaƙensa da waɗansu abubuwan da ya yi, suna a rubuce a littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
Le reste des actes de Jotham et tous ses combats, et tous ses errements sont d'ailleurs consignés dans le livre des rois d'Israël et de Juda.
8 Yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida.
Il avait vingt-cinq ans à son avènement et il régna seize ans à Jérusalem.
9 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Sai Ahaz ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Et Jotham reposa à côté de ses pères et reçut la sépulture dans la Cité de David. Et Achaz, son fils, devint roi en sa place.

< 2 Tarihi 27 >