< 2 Tarihi 22 >

1 Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
E os moradores de Jerusalém fizeram rei a Achazias, seu filho mais moço, em seu lugar: porque a tropa, que viera com os arabios ao arraial, tinha morto a todos os mais velhos: e assim reinou Achazias, filho de Jorão, rei de Judá.
2 Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
Era da idade de quarenta e dois anos, quando começou a reinar, e reinou um ano em Jerusalém: e era o nome de sua mãe Athalia, filha d'Omri.
3 Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
Também este andou nos caminhos da casa d'Achab; porque sua mãe era sua conselheira, para obrar impiamente.
4 Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
E fez o que era mal aos olhos do Senhor, como a casa d'Achab, porque eles eram seus conselheiros depois da morte de seu pai, para a sua perdição.
5 Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
Também andou no seu conselho, e foi-se com Jorão, filho d'Achab, rei de Israel, à peleja contra Hazael, rei da Síria, junto a Ramoth-gilead: e os siros feriram a Jorão,
6 saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
E tornou a curar-se em Jezreel, das feridas que se lhe deram junto a Rama, pelejando contra Hazael, rei da Síria: e Azarias, filho de Jorão, rei de Judá, desceu para ver a Jorão, filho d'Achab, em Jezreel; porque estava doente.
7 Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
Veio pois de Deus o abatimento d'Achazias, para que viesse a Jorão; porque vindo ele, saiu com Jorão contra Jehu, filho de Nimsi, a quem o Senhor tinha ungido para desarreigar a casa d'Achab.
8 Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
E sucedeu que, executando Jehu juízo contra a casa d'Achab, achou os príncipes de Judá e os filhos dos irmãos d'Achazias, que serviam a Achazias, e os matou.
9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
Depois buscou a Achazias (porque se tinha escondido em Samaria), e o alcançaram, e o trouxeram a Jehu, e o mataram, e o sepultaram; porque disseram: Filho é de Josaphat, que buscou ao Senhor com todo o seu coração. E não tinha já a casa d'Achazias ninguém que tivesse força para o reino.
10 Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
Vendo pois Athalia, mãe d'Achazias, que seu filho era morto, levantou-se, e destruiu, toda a semente real da casa de Judá.
11 Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
Porém Josebath, filha do rei, tomou a Joás, filho d'Achazias, e furtou-o dentre os filhos do rei, a quem matavam, e o pôs com a sua ama na câmara dos leitos: assim Josebath, filha do rei Jorão, mulher do sacerdote Joiada (porque era irmã d'Achazias), o escondeu de diante d'Athalia, de modo que o não matou.
12 Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
E esteve com eles escondido na casa de Deus seis anos: e Athalia reinou sobre a terra.

< 2 Tarihi 22 >