< 2 Tarihi 16 >

1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura don yă yaƙi Yahuda da Rama mai katanga, don kuma yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa sarkin Yahuda.
In the sixe and thirtieth yeere of the reigne of Asa came Baasha king of Israel vp against Iudah, and built Ramah to let none passe out or goe in to Asa king of Iudah.
2 Sai Asa ya ɗauki azurfa da zinariya daga ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma na fadansa ya aika wa Ben-Hadad sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
Then Asa brought out siluer and gold out of the treasures of the house of the Lord, and of the Kings house, and sent to Benhadad King of Aram that dwelt at Damascus, saying,
3 Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakani na da kai kamar yadda ya kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Dubi ina aika maka azurfa da zinariya. Yanzu ka yanke yarjejjeniya da Ba’asha sarkin Isra’ila domin yă janye daga gare ni.”
There is a couenant betweene me and thee, and betweene my father and thy father: behold, I haue sent thee siluer and golde: come, breake thy league with Baasha King of Israel that hee may depart from me.
4 Ben-Hadad ya yarda da Sarki Asa ya kuma aika da manyan hafsoshin mayaƙansa a kan garuruwan Isra’ila. Suka ci Iyon, Dan, Abel-Mayim da kuma dukan biranen ajiya na Naftali.
And Benhadad hearkened vnto King Asa, and sent the captaines of the armies which hee had, against the cities of Israel. And they smote Iion, and Dan, and Abel-maim, and all the store cities of Naphtali.
5 Da Ba’asha ya ji wannan, ya daina ginin Rama ya yashe aikinsa.
And when Baasha heard it, he left building of Ramah, and let his worke cease.
6 Sa’an nan Sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuda, suka kuma kwashe duwatsu da katako daga Rama waɗanda Ba’asha yake amfani da su. Da su ne Asa ya gina Geba da Mizfa.
Then Asa the King tooke all Iudah, and caryed away the stones of Ramah and the tymber thereof, wherewith Baasha did builde, and he built therewith Geba and Mizpah.
7 A lokacin Hanani mai duba ya zo wurin Asa sarkin Yahuda ya ce masa, “Don ka dogara ga sarkin Aram, ba kuwa ga Ubangiji Allahnka ba ne mayaƙan sarkin Aram sun kuɓuce daga hannunka.
And at that same time Hanani the Seer came to Asa King of Iudah, and saide vnto him, Because thou hast rested vpon the king of Aram, and not rested in the Lord thy God, therefore is the hoste of the King of Aram escaped out of thine hande.
8 Ai, Kushawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da kekunan yaƙi da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, ya kuwa ba da su cikin hannunka.
The Ethiopians and the Lubims, were they not a great hoste with charets and horsemen, exceeding many? yet because thou diddest rest vpon the Lord, he deliuered them into thine had.
9 Gama gaban Ubangiji yana ko’ina a duniya don yă ƙarfafa waɗanda zukatansu suke binsa cikin aminci. Ka yi wauta, daga yanzu nan gaba za ka yi ta yaƙi.”
For the eyes of the Lord beholde all the earth to shewe him selfe strong with them that are of perfite heart towarde him: thou hast then done foolishly in this: therefore from henceforth thou shalt haue warres.
10 Sai Asa ya yi fushi sosai da mai duban saboda wannan; ya yi fushi ƙwarai har ya sa aka jefa shi a kurkuku. A lokaci guda kuma Asa ya fara gwada wa mutane azaba.
Then Asa was wroth with the Seer, and put him into a prison: for he was displeased with him, because of this thing. And Asa oppressed certaine of the people at the same time.
11 Ayyukan mulkin Asa, daga farko zuwa ƙarshe, suna a rubuce a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
And behold, the actes of Asa first and last, loe, they are written in the booke of the Kings of Iudah and Israel.
12 A shekara ta talatin da tara ta mulkinsa, Asa ya kamu da wata cuta a ƙafarsa. Ko da yake cutar ta yi tsanani, duk d haka ma a cikin ciwonsa bai nemi taimako daga Ubangiji ba, sai dai daga likitoci.
And Asa in the nine and thirtieth yeere of his reigne was diseased in his feete, and his disease was extreme: yet he sought not the Lord in his disease, but to the Phisicions.
13 Sa’an nan a shekara ta arba’in da ɗaya ta mulkinsa, Asa ya mutu ya kuma huta tare da kakanninsa.
So Asa slept with his fathers, and dyed in the one and fourtieth yeere of his reigne.
14 Suka binne shi a kabarin da ya fafe wa kansa a Birnin Dawuda. Suka sa shi a makara wadda aka rufe da kayan yaji da kuma turare dabam-dabam da aka niƙa, suka kuma ƙuna babbar wuta don girmama shi.
And they buryed him in one of his sepulchres, which he had made for him selfe in the citie of Dauid, and layed him in the bed, which they had filled with sweete odours and diuers kindes of spices made by the arte of the apoticarie: and they burnt odours for him with an exceeding great fire.

< 2 Tarihi 16 >