< 2 Tarihi 12 >

1 Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
Lorsque Roboam eut affermi son royaume et acquis de la force, il abandonna la loi de Yahweh, et tout Israël avec lui.
2 Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
La cinquième année du règne de Roboam, Sésac, roi d'Egypte, monta contre Jérusalem, — parce qu'ils avaient péché contre Yahweh, —
3 Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
avec mille deux cents chars et soixante mille cavaliers; et l'on ne pouvait compter le peuple qui vint d'Egypte avec lui: Libyens, Sukkiens et Ethiopiens.
4 ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
Il prit les villes fortes qui appartenaient à Juda, et arriva jusqu'à Jérusalem.
5 Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
Sémaïas le prophète vint auprès de Roboam et des chefs de Juda qui s'étaient réunis dans Jérusalem à l'approche de Sésac, et il leur dit: " Ainsi dit Yahweh: Vous m'avez abandonné; moi aussi, je vous abandonne entre les mains de Sésac. "
6 Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
Les chefs d'Israël et le roi s'humilièrent et dirent: " Yahweh est juste! "
7 Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
Quand Yahweh vit qu'ils s'humiliaient, la parole de Yahweh fut adressée à Sémaïas en ces termes: " Ils se sont humiliés, je ne les détruirai point; dans un peu de temps je leur donnerai la délivrance, et ma colère ne se répandra pas sur Jérusalem par la main de Sésac.
8 Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
Mais ils lui seront assujettis, afin qu'ils sachent ce que c'est que me servir ou servir les royaumes des pays. "
9 Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
Sésac, roi d'Egypte, monta contre Jérusalem; il prit les trésors de la maison de Yahweh et les trésors de la maison du roi: il prit tout. Il prit les boucliers d'or que Salomon avait faits.
10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
A leur place, le roi Roboam fit des boucliers d'airain, et il les remit aux mains des chefs des coureurs qui gardaient l'entrée de la maison du roi.
11 Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
Chaque fois que le roi allait à la maison de Yahweh, les coureurs venaient et les portaient; et ils les rapportaient ensuite dans la chambre des coureurs.
12 Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
Comme Roboam s'était humilié, la colère de Yahweh se détourna de lui, de sorte qu'il ne fut pas détruit entièrement; et il y eut encore des choses bonnes en Juda.
13 Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
Le roi Roboam s'affermit dans Jérusalem et régna. Il avait quarante et un ans lorsqu'il devint roi, et il régna dix-sept ans à Jérusalem, ville que Yahweh avait choisie parmi toutes les tribus d'Israël pour y mettre son nom. Sa mère s'appelait Naama, l'Ammonite.
14 Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
Il fit le mal, parce qu'il n'appliqua pas son cœur à chercher Yahweh.
15 Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Les actes de Roboam, les premiers et les derniers, ne sont-ils pas écrits dans les Paroles de Séméïas le prophète et dans celles d'Addo le voyant concernant les généalogies? Il y eut toujours des guerres entre Roboam et Jéroboam.
16 Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.
Roboam se coucha avec ses pères, et il fut enterré dans la ville de David. Abia, son fils, régna à sa place.

< 2 Tarihi 12 >