< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Torej tam je bil mož iz Benjamina, katerega ime je bilo Kiš, sin Abiéla, sinú Cerórja, sinú Behoráta, sinú Afíaha, Benjaminovec, mogočen človek moči.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
Imel je sina, čigar ime je bilo Savel, izbranega in čednega mladeniča in med Izraelovimi otroki ni bilo čednejše osebe kakor on. Od njegovih ramen in navzgor je bil višji kakor katerikoli izmed ljudstva.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
Oslice Savlovega očeta Kiša so se izgubile. Kiš je rekel svojemu sinu Savlu: »Vzemi torej s seboj enega izmed služabnikov in vstani, pojdi iskat oslice.«
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
Prečkal je goro Efrájim in šel skozi deželo Šalíša, toda nista jih našla. Potem sta šla skozi deželo Šaalím in tam jih ni bilo. Šel je skozi deželo Benjaminovcev, toda nista jih našla.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
In ko sta prišla do dežele Cuf, je Savel rekel svojemu služabniku, ki je bil z njim: »Pridi in se vrniva, da ne bi moj oče prenehal skrbeti za oslice in bi mislil na naju.«
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
Rekel mu je: »Glej torej, v tem mestu je Božji mož in ta je častitljiv mož. Vse, kar reče, se zagotovo zgodi. Pojdiva sedaj tja, morda nama on lahko pokaže pot, po kateri naj greva.«
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
Potem je Savel rekel svojemu služabniku: »Toda glej, če greva, kaj bova prinesla možu? Kajti kruh v najinih posodah je pošel in ni darila, da bi ga prinesla Božjemu možu. Kaj imava?«
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
Služabnik je ponovno odgovoril Savlu in rekel: »Glej, tukaj pri roki imam četrtinko šekla srebra. To bom dal Božjemu možu, da nama pove najino pot.«
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
(Poprej je v Izraelu mož, ko je šel, da poizveduje od Boga, govoril tako: »Pridite in pojdimo k vidcu, « kajti kdor je sedaj imenovan prerok, je bil poprej imenovan videc.)
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Potem je Savel rekel svojemu služabniku: »Dobro rečeno. Pridi, pojdiva.« Tako sta šla v mesto, kjer je bil Božji mož.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
In ko sta šla gor, po hribu do mesta, sta našla mladenke, ki so prihajale ven, da zajamejo vodo in rekla sta jim: »Je tukaj videc?«
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
Odgovorile so jima in rekle: »Je, glejta, pred vama je. Sedaj pohitita, kajti danes je prišel v mesto, kajti danes je klavna daritev ljudstva na visokem kraju.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
Takoj ko prideta v mesto, ga bosta nemudoma našla, preden gre gor na visok kraj, da jé, kajti ljudstvo ne bo jedlo, dokler on ne pride, ker on blagoslovi klavno daritev in potem tisti, ki so povabljeni, jedo. Sedaj torej pojdita gor, kajti približno ta čas ga bosta našla.«
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
Šla sta gor v mesto in ko sta prišla v mesto, glej, je Samuel prihajal ven proti njima, da bi šel gor na visok kraj.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
Torej Gospod je Samuelu na uho povedal, dan poprej, preden je Savel prišel, rekoč:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
»Jutri okrog tega časa ti bom poslal moža iz Benjaminove dežele in ti ga boš mazilil, da bo poveljnik nad mojim ljudstvom Izraelom, da bo lahko rešil moje ljudstvo iz roke Filistejcev, kajti jaz sem pogledal na svoje ljudstvo, ker je njihov krik prišel k meni.«
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
Ko je Samuel zagledal Savla, mu je Gospod rekel: »Glej mož, o katerem sem ti govoril! Ta isti bo kraljeval nad mojim ljudstvom.«
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Potem se je Savel približal k Samuelu v velikih vratih in rekel: »Povej mi, prosim te, kje je vidčeva hiša.«
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
Samuel je odgovoril Savlu in rekel: »Jaz sem videc. Pojdi gor pred menoj na visok kraj, kajti danes boš jedel z menoj, jutri pa te bom pustil oditi in povedal ti bom vse, kar je v tvojem srcu.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
Glede oslic, ki so bile izgubljene pred tremi dnevi, ne naravnaj svojih misli nanje, kajti najdene so. Na kom je vse hrepenenje Izraela? Ali ni na tebi in na vsej hiši tvojega očeta?«
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
Savel je odgovoril in rekel: » Ali nisem Benjaminovec, od najmanjšega izmed Izraelovih rodov? In moja družina najmanjša izmed vseh družin Benjaminovega rodu? Zakaj mi potem tako govoriš?«
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
Samuel je vzel Savla in njegovega služabnika ter ju privedel v dvorano in ju primoral sesti na najvišje mesto med tistimi, ki so bili povabljeni, katerih je bilo približno trideset oseb.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
Samuel je rekel kuharju: »Prinesi delež, ki sem ti ga dal, od katerega sem ti rekel: ›Postavi to poleg sebe.‹«
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
Kuhar je vzel pleče in tisto, kar je bilo na njem in to postavil pred Savla. Samuel je rekel: »Glej to, kar je preostalo! Postavi to predse in jej, kajti za ta čas je bilo prihranjeno zate, odkar sem rekel: ›Povabil sem ljudstvo.‹« Tako je Savel tisti dan jedel s Samuelom.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
Ko sta prišla dol iz visokega kraja v mesto, se je Samuel s Savlom posvetoval na vrhu hiše.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
Zgodaj so vstali in pripetilo se je ob svitanju dneva, da je Samuel poklical Savla na vrhu hiše, rekoč: »Vstani, da te lahko odpošljem.« Savel je vstal in odšla sta ven, oba izmed njiju, on in Samuel.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
In ko sta se spuščala dol, do konca mesta, je Samuel rekel Savlu: »Zapovej služabniku, da gre naprej pred nama (in ta je šel naprej), toda ti malce postoj, da ti lahko pokažem besedo od Boga.«

< 1 Sama’ila 9 >