< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
There was nowe a man of Beniamin, mightie in power named Kish, the sonne of Abiel, the sonne of Zeror, the sonne of Bechorath, the sonne of Aphiah, the sonne of a man of Iemini.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
And he had a sonne called Saul, a goodly yong man and a faire: so that among the children of Israel there was none goodlier then he: from the shoulders vpwarde he was hier then any of the people.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
And the asses of Kish Sauls father were lost: therefore Kish said to Saul his sonne, Take nowe one of the seruants with thee, and arise, goe, and seeke the asses.
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
So he passed through mount Ephraim, and went through the lande of Shalishah, but they found them not. Then they went through the land of Shalim, and there they were not: he went also through ye land of Iemini, but they found the not.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
When they came to the lande of Zuph, Saul saide vnto his seruant that was with him, Come and let vs returne, lest my father leaue the care of asses, and take thought for vs.
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
And he said vnto him, Behold nowe, in this citie is a man of God, and he is an honorable man: all that he saith commeth to passe: let vs nowe goe thither, if so be that he can shewe vs what way we may goe.
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
Then saide Saul to his seruant, Well then, let vs goe: but what shall we bring vnto the man? For the bread is spent in our vessels, and there is no present to bring to the man of God: what haue we?
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
And the seruant answered Saul againe, and said, Beholde, I haue founde about me the fourth part of a shekell of siluer: that will I giue the man of God, to tell vs our way.
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
(Beforetime in Israel when a man went to seeke an answere of God, thus he spake, Come, and let vs goe to the Seer: for he that is called nowe a Prophet, was in the olde time called a Seer)
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Then saide Saul to his seruant, Well saide, come, let vs goe: so they went into the citie where the man of God was.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
And as they were going vp the hie way to the citie, they found maydes that came out to draw water, and said vnto them, Is there here a Seer?
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
And they answered them, and said, Yea: loe, he is before you: make haste nowe, for he came this day to the citie: for there is an offering of the people this day in the hie place.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
When ye shall come into the citie, ye shall finde him straightway yet he come vp to the hie place to eate: for the people will not eate vntill he come, because he will blesse the sacrifice: and then eate they that be bidden to the feast: nowe therefore goe vp: for euen now shall ye find him.
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
Then they went vp into the citie, and when they were come into the middes of the citie, Samuel came out against them, to goe vp to the hie place.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
But the Lord had reueiled to Samuel secretly (a day before Saul came) saying,
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
To morow about this time I will send thee a man out of the land of Beniamin: him shalt thou anoint to be gouernour ouer my people Israel, that he may saue my people out of the hands of the Philistims: for I haue looked vpon my people, and their crie is come vnto me.
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
When Samuel therefore sawe Saul, the Lord answered him, See, this is the man whom I spake to thee of, he shall rule my people.
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Then went Saul to Samuel in the middes of the gate, and said, Tell me, I pray thee, where the Seers house is.
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
And Samuel answered Saul, and saide, I am the Seer: goe vp before me vnto the hie place: for ye shall eate with me to day. and to morowe I will let thee goe, and will tell thee all that is in thine heart.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
And as for thine asses that were lost three dayes ago, care not for them: for they are founde. and on whom is set all the desire of Israel? is it not vpon thee and on all thy fathers house?
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
But Saul answered, and said, Am not I the sonne of Iemini of the smallest tribe of Israel? and my familie is the least of all the families of the tribe of Beniamin. Wherefore then speakest thou so to me?
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
And Samuel tooke Saul and his seruant, and brought them into the chamber, and made them sit in the chiefest place among them that were bidden: which were about thirtie persons.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
And Samuel saide vnto the cooke, Bring foorth the portion which I gaue thee, and whereof I said vnto thee, Keepe it with thee.
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
And the cooke tooke vp the shoulder, and that which was vpon it, and set it before Saul. And Samuel said, Beholde, that which is left, set it before thee and eate: for hitherto hath it bene kept for thee, saying, Also I haue called the people. So Saul did eate with Samuel that day.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
And when they were come downe from the hie place into the citie, he communed with Saul vpon the top of the house.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
And when they arose early about ye spring of the day, Samuel called Saul to the top of the house, saying, Vp, that I may send thee away. And Saul arose, and they went out, both he, and Samuel.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
And when they were come downe to the ende of the citie, Samuel said to Saul, Bid the seruant goe before vs, (and he went) but stand thou still nowe, that I may shewe thee the worde of God.

< 1 Sama’ila 9 >