< 1 Sama’ila 5 >

1 Bayan Filistiyawa sun ƙwace akwatin alkawarin Allah, sai suka ɗauke shi daga Ebenezer suka kai shi Ashdod.
Now, the Philistines, having taken the ark of God, —brought it in from Eben-ezer, unto Ashdod.
2 Sa’an nan suka ɗauki akwatin alkawarin suka kai shi cikin haikalin gunkinsu Dagon, suka ajiye kusa da Dagon.
And, when the Philistines took the ark of God, they brought it into the house of Dagon, —and placed it by the side of Dagon.
3 Kashegari da safe da mutanen Ashdod suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Sai suka ɗauki Dagon suka ajiye a wurin zamansa.
And, when they of Ashdod rose early on the morrow and entered into the house of Dagon, they looked and lo! Dagon, was lying prostrate on his face to the earth, before the ark of Yahweh, —so they took Dagon and restored him to his place.
4 Amma kashegari kuma da safe suka farka sai ga Dagon ya fāɗi a ƙasa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji! Kansa ya fashe, hannuwansa kuma sun kakkarye sun zube a madogarar ƙofa; jikinsa ne kaɗai ya rage.
And, when they rose up early in the morning of the morrow, lo! Dagon, was lying prostrate on his face to the earth, before the ark of Yahweh—and, the head of Dagon, and both the palms of his hands, had been cut off against the threshold, only, Dagon himself, was left to him.
5 Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba sa taka bakin ƙofar Dagon a Ashdod har wa yau.
For this cause, do not the priests of Dagon, nor any that enter into the house of Dagon, tread upon the threshold of Dagon, in Ashdod, —until this day.
6 Hannun Ubangiji kuwa ya yi nauyi a bisa Ashdod da kewayenta. Ya kawo hallaka ga dukansu, ya kuma buga su da marurai.
Then was the hand of Yahweh heavy against them of Ashdod, and he astounded them, —and smote with tumours Ashdod and her bounds.
7 Da mutanen Ashdod suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Lalle Akwatin Alkawarin Allah na Isra’ila ba zai kasance da mu ba, domin hannunsa yana da nauyi a kanmu da bisan Dagon allahnmu.”
And, when the men of Ashdod saw that, so, it was, then kept they saying, Let not the ark of the God of Israel abide with us, for, hard, is his hand upon us, and upon Dagon our god.
8 Saboda haka suka kira duka shugabannin Filistiyawa suka tambaye su, suka ce, “Me za mu da akwatin alkawarin Allahn Isra’ila?” Sai suka amsa suka ce, “A ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila a kai shi Gat.” Sai suka ɗauki akwatin alkawarin Allah na Isra’ila.
So they sent and gathered together all the lords of the Philistines unto them, and said—What shall we do with the ark of the God of Israel? And they said: To Gath, let the ark of the God of Israel go round. So they took round the ark of the God of Israel.
9 Amma bayan sun kai shi can, sai hannun Ubangiji ya yi gāba da birnin, aka jefa shi cikin wani mawuyacin hali. Ya buga mutanen birnin da marurai, babba da yaro.
And so it was, after they had taken it round, then was the hand of Yahweh against the city, with an exceeding great consternation, and he smote the men of the city, from the least, even unto the greatest, —and they brake out with tumours.
10 Sai suka aika da akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Yayinda akwatin alkawarin Allah yana shiga cikin Ekron, mutanen Ekron suka yi ihu, suka ce, “An kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra’ila domin yă kashe mu da mutanenmu.”
Then sent they the ark of God to Ekron, —and so it was, when the ark of God entered Ekron, that the Ekronites made outcry, saying—They have brought round unto me the ark of the God of Israel, to slay me, and my people!
11 Saboda haka suka kira ga dukan shugabannin Filistiyawa suka ce, “Ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila inda ya fito; in ba haka ba zai kashe mu da mutanenmu.” Gama mutuwa ta cika garin da tsoro. Hannun Allah ya yi nauyi a kansa.
So they sent and gathered together all the lords of the Philistines, and said—Send away the ark of the God of Israel, and restore it to its own place, that it slay not me, and my people. For there had come a deadly consternation, throughout all the city, heavy exceedingly, was the hand of God there.
12 Waɗanda ba su mutu ba kuwa, sun kamu da marurai. Kukan birnin kuwa ta hau har zuwa sama.
And, the men who died not, were smitten with the tumours, —so the cry of the city for help, ascended the heavens.

< 1 Sama’ila 5 >