< 1 Sama’ila 2 >

1 Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
И помолися Анна и рече: утвердися сердце мое в Господе, вознесеся рог мой в Бозе моем, разширишася уста моя на враги моя, возвеселихся о спасении Твоем:
2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
яко несть свят яко Господь, и несть праведен яко Бог наш, и несть свят паче Тебе:
3 “Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
не хвалитеся и не глаголите высокая в гордыни, ниже да изыдет велеречие из уст ваших: яко Бог разумов Господь, и Бог уготовляяй начинания Своя:
4 “An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
лук сильных изнеможе, и немощствующии препоясашася силою:
5 Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
исполненнии хлеба лишишася, и алчущии пришелствоваша землю: яко неплоды роди седмь, и многая в чадех изнеможе:
6 “Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol h7585)
Господь мертвит и живит, низводит во ад и возводит, (Sheol h7585)
7 Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
Господь убожит и богатит, смиряет и высит,
8 Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
возставляет от земли убога и от гноища воздвизает нища посадити его с могущими людий, и престол славы дая в наследие им:
9 Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
даяй молитву молящемуся и благослови лета праведнаго, яко не в крепости силен муж:
10 waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
Господь немощна сотвори сопостата Его, Господь свят: да не хвалится премудрый премудростию своею, и да не хвалится сильный силою своею, и да не хвалится богатый богатством своим: но о сем да хвалится хваляйся, еже разумети и знати Господа, и творити суд и правду посреде земли: Господь взыде на небеса и возгреме: той судит концем земли, праведен сый, и даст крепость царем нашым и вознесет рог христа Своего.
11 Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
И оставиша его тамо пред Господем и отидоша во Армафем в дом свой: отроча же бе служа лицу Господню пред лицем Илии жерца.
12 ’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
Сынове же Илии жерца (быша) сынове погибелнии, не ведуще Господа,
13 Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
ни оправдания жреческа пред людьми всеми жрущими. И прихождаше отрок жреческ, егда варятся мяса, и удица трезубна в руку его,
14 zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
и влагаше ю в коноб великий, или в медяный сосуд, или горнец, и все еже вонзеся на удицу, взимаше е себе жрец: и тако творяху всему Израилеви приходящему пожрети Господеви в Силоме.
15 Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
И прежде каждения тука, прихождаше отрок жреческ и глаголаше мужеви жрущему: даждь мяса испещи жерцу, и не возму от тебе мяса варенаго от коноба.
16 In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
И глаголаше муж жряй: да покадится первее тук, якоже подобает, и тогда возмеши себе от всех, еже хощет душа твоя. И рече: ни, ныне даждь: аще же не даси, возму силою.
17 Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
И бе пред Господем грех отроков велий зело, яко отметаху жертву Господню.
18 Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
И Самуил бе служа пред Господем, отрочищь сый опоясан во ефуд льнян.
19 Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
И хламиду малу сотвори ему мати его, и приношаше ему от дний во дни, егда восхождаше с мужем своим пожрети жертву дний.
20 Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
И благослови Илий Елкану и жену его, глаголя: да воздаст ти Господь семя от жены сея за дар, егоже даровал еси Господеви. И отиде человек в место свое.
21 Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
И посети Господь Бог Анну, и зача, и роди еще три сыны и дщери две. И возвеличися отрок Самуил пред Господем.
22 To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
Илий же состареся зело: и услыша, яже творяху сынове его всем сыном Израилевым, и яко бываху с женами предстоящими у дверий скинии свидения,
23 Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
и рече им: почто творите по глаголу сему, егоже аз слышу из уст всех людий Господних (о вас)?
24 A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
Ни, чада, ни: яко не благ слух, егоже аз слышу о вас: не творите тако, яко не добры слухи, яже аз слышу, еже не работати людем Богу:
25 In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
аще согрешая согрешит муж мужеви, помолятся о нем ко Господу: аще же Господеви согрешит, кто помолится о нем? И не послушаста гласа отца своего, яко хотяй восхоте Господь погубити я.
26 Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
Отрок же Самуил хождаше предуспевая, и бе благ пред Господем и человеки.
27 Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
И прииде человек Божий ко Илию и рече: сия глаголет Господь: открываяся открыхся в дому отца твоего, сущым им в земли Египетстей рабом в дому фараони,
28 Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
и избрах дом отца твоего от всех домов Израилевых Мне служити, еже восходити ко олтарю Моему и кадити кадилом и носити ефуд, и дах дому отца твоего вся, яже огня жертвенная сынов Израилевых, в снедь:
29 Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
и почто ты воззрел еси на фимиам Мой и на жертву Мою безстудным оком, и прославил сыны твоя паче Мене, еже благословляти начаток всякия жертвы Израилевы предо Мною?
30 “Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
Сего ради сия глаголет Господь Бог Израилев, глаголя: рекох, дом твой и дом отца твоего прейдет предо Мною до века: а ныне глаголет Господь: никакоже Мне, зане токмо прославляющыя Мя прославлю, и уничижаяй Мя безчестен будет:
31 Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
се, дние идут, и потреблю семя твое и семя дому отца твоего, и не будет старца в дому твоем во вся дни,
32 Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
и узриши державу Мою во всех, имиже разблажает Израиля, и не будет старца в дому твоем во вся дни:
33 Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
и мужа не истреблю тебе от олтаря Моего, во еже оскудети очесем его и истаяти души его: и вси прочии дому твоего падут оружием мужеским:
34 “‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
и сие тебе знамение, еже приидет на оба сына твоя сия Офни и Финееса: в день един умрут оба:
35 Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
и возставлю Себе жерца верна, иже вся яже в сердцы Моем и яже в души Моей сотворит, и созижду ему дом верен, и предидет пред христом Моим во вся дни:
36 Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”
и будет всяк оставшийся в дому твоем приидет поклонитися ему с цатою сребра и хлебом единым, глаголя: приими мя к единому от священнослужений твоих, еже ясти хлеб.

< 1 Sama’ila 2 >