< 1 Sama’ila 14 >

1 Wata rana Yonatan ɗan Shawulu ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo mu tafi wajen sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai gaya wa mahaifinsa ba.
One day, Jonathan son of Saul said to his young armor bearer, “Come, let us go over to the Philistines' garrison on the other side.” But he did not tell his father.
2 Shawulu kuwa na zaune a gindin itacen rumman a bayan garin Gibeya a Migron. Tare da shi akwai mutum wajen ɗari shida.
Saul was staying on the outskirts of Gibeah under the pomegranate tree that is in Migron. About six hundred men were with him,
3 A cikinsu akwai Ahiya sanye da efod. Shi yaron Ikabod ɗan’uwan Ahitub ne, ɗan Finehas, ɗan Eli, firist na Ubangiji a Shilo. Ba wanda ya san cewa Yonatan ya tafi wani wuri.
including Ahijah son of Ahitub (Ichabod's brother) son of Phinehas son of Eli, the priest of Yahweh at Shiloh, who wore an ephod. The people did not know that Jonathan was gone.
4 A kowane gefe na mashigin da Yonatan ya so yă bi zuwa wurin Filistiyawa, akwai hawa mai tsawo, ana kira ɗaya Bozez, ɗayan kuma ana kira Senet.
On each side of the pass through which Jonathan wanted to go in order to get to the Philistines' garrison, there was a rocky cliff on one side and another rocky cliff on the other side. One rocky cliff was called Bozez and the other rocky cliff was called Seneh.
5 Hawan da yake arewa yana fuskantar Mikmash, wanda yake kudu kuma yana fuskantar Geba.
One rocky cliff stood on the north in front of Michmash, and the other on the south in front of Geba.
6 Yonatan ya ce wa saurayin mai ɗaukan makamai, “Zo mu haye zuwa mashigin mutane marasa kaciyan nan, wataƙila Ubangiji zai yi aiki a madadinmu. Ba abin da zai iya hana Ubangiji yin aikin ceto ta wurin mutane masu yawa, ko ta wurin mutane kaɗan.”
Jonathan said to his young armor bearer, “Come, let us cross over to the garrison of these uncircumcised fellows. It may be that Yahweh will work on our behalf, for nothing can stop Yahweh from saving by many or by few people.”
7 Mai ɗaukan makaman ya ce, “Ka yi duk abin da yake zuciyarka. Ci gaba, ina tare da kai gaba da baya.”
His armor bearer replied, “Do everything that is in your heart. Go ahead, see, I am with you, to obey all your commands.”
8 Yonatan ya ce, “To, zo mu haye zuwa wajen mutanen, mu sa su gan mu.
Then Jonathan said, “We will cross over to the men, and we will show ourselves to them.
9 In suka ce mana, ‘Ku tsaya nan har mu zo wurinku,’ za mu dakata inda muke, ba za mu haura wajensu ba.
If they say to us, 'Wait there until we come over to you'—then we will stay in our place and will not cross over to them.
10 Amma in suka ce mana, ‘Ku haura wurinmu,’ to, sai mu haura, wannan zai zama mana alama cewa Ubangiji ya bashe su a hannunmu.”
But if they reply, 'Come over to us,' then we will cross over; because Yahweh has given them into our hand. This will be the sign to us.”
11 Sai suka nuna kansu a sansanin Filistiyawa. Sai Filistiyawa suka ce, “Ku duba ga Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.”
So both of them revealed themselves to the garrison of the Philistines. The Philistines said, “Look, Hebrews are coming out of the holes where they have hidden themselves.”
12 Mutanen da suke sansanin suka kira Yonatan da mai ɗaukan makamansa da babbar murya suka ce, “Ku hauro wajenmu, mu kuwa za mu koya muku hankali.” Sai Yonatan ya ce wa mai ɗaukan makamansa, “Biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra’ila.”
Then the men of the garrison called to Jonathan and his armor bearer, and said, “Come up to us, and we will show you something.” Jonathan said to his armor bearer, “Follow after me, because Yahweh has given them into the hand of Israel.”
13 Sai Yonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukan makamansa kuwa yana biye. Yonatan ya yi ta fyaɗa Filistiyawa da ƙasa, mai ɗaukan makamansa kuma ya yi ta karkashe su.
Jonathan climbed up on his hands and feet, and his armor bearer followed behind him. The Philistines were put to death before Jonathan, and his armor bearer put some to death behind him.
14 A wannan karo na farko Yonatan da mai ɗaukan makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi rabin kadada.
That first attack that Jonathan and his armor bearer made, killed about twenty men within an area of half an acre.
15 Sai tsoro ya kama dukan sojojin Filistiyawa, waɗanda suke cikin sansanin da waɗanda suke fili, har da waɗanda suke waje, da kuma waɗanda suke kai hari, ƙasa ta girgiza. Allah ne ya kawo wannan rikicewa.
There was a panic in the camp, in the field, and among the people. Even the garrison and the raiders panicked. The earth quaked, and there was a great panic.
16 Masu gadin Shawulu a Gebiya da take a Benyamin suka duba sai ga rundunar Filistiyawa a warwatsewa ko’ina.
Then Saul's watchmen in Gibeah of Benjamin looked; the crowd of Philistine soldiers was dispersing, and they were going here and there.
17 Sai Shawulu ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ku ƙidaya mayaƙa ku ga wane ne ba ya nan.” Da suka ƙirga sai suka tarar Yonatan da mai ɗaukan makamansa ba sa nan.
Then Saul said to the people that were with him, “Count and see who is missing from us.” When they had counted, Jonathan and his armor bearer were missing.
18 Shawulu ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah.” (A lokacin akwatin alkawarin yana tare da Isra’ilawa.)
Saul said to Ahijah, “Bring the ark of God here,” for at that time it was with the people of Israel.
19 Yayinda Shawulu yake magana da firist kuwa, harguwa ya yi ta ƙaruwa a sansanin Filistiyawa. Sai Shawulu ya ce wa firist, “Janye hannunka.”
While Saul was talking to the priest, the commotion in the camp of the Philistines was continuing and increasing. Then Saul said to the priest, “Withdraw your hand.”
20 Sa’an nan Shawulu da dukan mutanensa suka taru suka tafi yaƙi. Suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna yaƙi da juna da takubansu.
Saul and all the people who were with him rallied and went into battle. Every Philistine's sword was against his fellow countrymen, and there was very great confusion.
21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi Filistiyawan zuwa sansanin yaƙinsu, suka juya, suka goyi bayan Shawulu da Yonatan sa’ad da yaƙin ya taso.
Now those Hebrews who previously had been with the Philistines, and who had gone with them into the camp, even they joined with the Israelites that were with Saul and Jonathan.
22 Sa’ad da dukan Isra’ilawan da suka ɓuya a duwatsu a ƙasar Efraim suka ji labari cewa Filistiyawa suna gudu, sai suka fito suka fafare su.
When all the men of Israel who had hidden themselves in the hills near Ephraim heard that the Philistines were fleeing, even they chased after them in battle.
23 Haka Ubangiji ya kuɓutar da Isra’ila a wannan rana. Yaƙin kuwa ya ci gaba har gaba da Bet-Awen.
So Yahweh saved Israel that day, and the battle passed beyond Beth Aven.
24 A wannan rana, Isra’ilawa suka sha wahala ƙwarai domin Shawulu ya sa mutane suka yi rantsuwa cewa, “La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana, kafin in ɗauki fansa a kan abokan gābana.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci.
That day the men of Israel were distressed because Saul had put the people under an oath and said, “Cursed be the man that eats any food until evening and I am avenged on my enemies.” So none of the troops tasted food.
25 Dukan rundunar ta shiga kurmi, sai ga zuma a ƙasa.
Then all the people entered the forest and there was honey upon the ground.
26 Da suka shiga ciki kurmin, suka ga zuma tana zubowa, duk da haka ba wanda ya sa yatsansa ya lasa saboda tsoron rantsuwar da suka yi.
When the people entered into the forest, the honey flowed, but no one put his hand to his mouth for the people feared the oath.
27 Yonatan bai san cewa mahaifinsa ya sa mutane suka yi rantsuwa ba. Sai ya sa gindin sandan da yake hannunsa a saƙar zuma, ya kai bakinsa. Nan da nan sai ya ji ƙarfin jiki ya zo masa.
But Jonathan had not heard that his father had bound the people with an oath. He reached out the tip of the staff that was in his hand and dipped it in the honeycomb. He raised his hand to his mouth, and his eyes brightened.
28 Sai wani soja ya gaya masa cewa, “Mahaifinka ya sa kowa ya yi rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin fāɗuwar rana!’ Shi ya sa duk sojojin ba su da ƙarfi.”
Then one of the people, answered, “Your father strictly charged the people with an oath, by saying, 'Cursed be the man that eats food on this day,' even though the people are weak from hunger.”
29 Yonatan ya ce, “Mahaifina ya jefa ƙasar cikin matsala. Duba yadda na ji ƙarfin jiki sa’ad da na ɗanɗana wannan’yar zuma mana.
Then Jonathan said, “My father has made trouble for the land. See how my eyes have become brightened because I tasted a little of this honey.
30 Da yaya zai kasance ke nan da a ce an bar sojoji suka ci abincin da suka ƙwace daga abokan gābansu? Ai, da gawawwakin Filistiyawan da aka kashe sun fi haka.”
How much better if the people had eaten freely today of the plunder from their enemies that they found? Because now the slaughter has not been great among the Philistines.”
31 A ranan nan Isra’ilawa suka yi ta kashe Filistiyawa daga Mikmash har zuwa Aiyalon. Bayan haka gajiya ta kama su sosai saboda yunwa.
They attacked the Philistines that day from Michmash to Aijalon. The people were very weary.
32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yayyanka su, suka ci naman ɗanye.
The people rushed greedily on the plunder and took sheep, oxen and calves, and killed them on the ground. The people ate them with the blood.
33 Sai wani mutum ya ce wa Shawulu, “Duba, ga mutane suna zunubi ga Ubangiji, suna cin nama da jini.” Shawulu ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse zuwa wurina nan da nan.”
Then they told Saul, “Look, the people are sinning against Yahweh by eating with the blood.” Saul said, “You have acted unfaithfully. Now, roll a big stone here to me.”
34 Sa’an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama’a duka, su kawo shanu da tumaki a nan, su yayyanka, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Haka nan kowa ya kawo saniyarsa a daren, ya yanka a can.
Saul said, “Go out among the people, and tell them, 'Let every man bring his ox and his sheep, kill them here, and eat. Do not sin against Yahweh by eating with the blood.'” So each of the people brought his own ox with him that night and killed it there.
35 Sa’an nan Shawulu ya gina wa Ubangiji bagade. Wannan ne bagade na farkon da ya gina.
Saul built an altar to Yahweh, which was the first altar that he built to Yahweh.
36 Shawulu ya ce, “Mu bi gangara mu fafare Filistiyawa da dare mu washe su har gari yă waye, mu kuma karkashe kowannensu, kada mu bar wani da rai.” Suka ce, “Ka yi duk abin da ka ga ya fi maka kyau.” Amma firist ya ce, “Bari mu nemi nufin Allah tukuna.”
Then Saul said, “Let us pursue the Philistines by night and plunder them until morning; let us not leave one of them alive.” They replied, “Do whatever seems good to you.” But the priest said, “Let us approach God here.”
37 Saboda haka Shawulu ya tambayi Allah ya ce, “Mu bi bayan Filistiyawa? Za ka bashe su a hannun Isra’ila?” Amma Allah bai ba shi amsa a ranar ba.
Saul asked God, “Should I pursue the Philistines? Will you give them into the hand of Israel?” But God did not answer him that day.
38 Saboda haka Shawulu ya ce, “Ku zo nan dukanku shugabannin rundunoni, mu bincika mu san zunubin da ya kawo rashin amsan nan yau.
Then Saul said, “Come here, all you leaders of the people; learn and see how this sin has happened today.
39 Muddin Ubangiji wanda ya ceci Isra’ila yana raye, ko da ɗana Yonatan ne ya yi zunubin, dole yă mutu.” Amma ba ko ɗaya daga cikinsu da ya ce uffam.
For, as Yahweh lives, who saves Israel, even if it is in Jonathan my son, he will surely die.” But none of the men among all the people answered him.
40 Sai Shawulu ya ce wa dukan Isra’ilawa, “Ku tsaya a can, ni kuma da Yonatan ɗana mu tsaya a nan.” Mutanen suka ce, “Ka yi abin da ya fi maka kyau.”
Then he said to all Israel, “You must stand on one side, and I and Jonathan my son will be on the other.” The people said to Saul, “Do what seems good to you.”
41 Sa’an nan Shawulu ya yi addu’a ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, “Me ya sa ba ka amsa mini addu’ata a yau ba? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Yonatan, ka nuna mana ta wurin Urim, amma idan laifin mutanen ne ka amsa ta wurin Tummim.” Ba a sami mutane da laifi ba, amma ƙuri’a ta fāɗa a kan Yonatan da Shawulu.
Saul said, “Yahweh, God of Israel! If this sin has been committed by me or by my son Jonathan, then, Yahweh, God of Israel, give the Urim. But if this sin has been committed by your people Israel, give the Thummim.” Then Jonathan and Saul were taken by lot, but the army was exonerated.
42 Shawulu ya ce, “Ku jefa ƙuri’a tsakanina da ɗana Yonatan.” Sai ƙuri’ar ta fāɗa a kan Yonatan.
Then Saul said, “Cast lots between me and Jonathan my son.” Then Jonathan was taken by lot.
43 Sai Shawulu ya ce wa Yonatan, “Gaya mini mene ne ka yi.” Yonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana zuma kaɗan daga gindin sandanta. Yanzu kuwa dole in mutu!”
Then Saul said to Jonathan, “Tell me what you have done.” Jonathan told him, “I tasted a little honey with the end of the rod that was in my hand. Here I am; I will die.”
44 Shawulu ya ce, “Bari hukunci mai tsanani na Allah yă kasance a kaina, in ba ka mutu ba, Yonatan.”
Saul said, “God do so and more also to me, if you do not die, Jonathan.”
45 Amma mutane suka ce wa Shawulu, “A ce Yonatan yă mutu bayan shi ya kawo babban nasara a Isra’ila? Faufau, muddin Ubangiji yana raye, ko gashin kansa ɗaya ba zai fāɗi a ƙasa ba, gama abin da ya yi yau, Allah ne yana tare da shi.” Ta haka mutane suka ceci Yonatan daga mutuwa.
Then the people said to Saul, “Should Jonathan die, who has accomplished this great victory for Israel? Far from it! As Yahweh lives, not one hair of his head will fall to the ground, for he has worked with God today.” So the people rescued Jonathan so that he did not die.
46 Sai Shawulu ya daina bin Filistiyawa, suka koma ƙasarsu.
Then Saul stopped pursuing the Philistines, and the Philistines went to their own place.
47 Bayan Shawulu ya hau karagar mulkin Isra’ila, ya yi yaƙi da abokan gābansu ta kowane gefe. Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, sarakunan Zoba, da kuma Filistiyawa. Duk wurin da ya juya, ya hore su.
When Saul began to rule over Israel, he fought against all his enemies on every side. He fought against Moab, the Ammonites, Edom, the kings of Zobah, and the Philistines. Wherever he turned, he inflicted punishment on them.
48 Ya yi jaruntaka sosai, ya ci Amalekawa da yaƙi, ya kuma ceci Isra’ila daga hannuwan waɗanda suka ƙwace musu kaya.
He acted with great courage and defeated the Amalekites. He rescued Israel out of the hands of those who plundered them.
49 ’Ya’yan Shawulu maza su ne, Yonatan, Ishbi, da Malki-Shuwa. Sunan babban’yarsa ita ce Merab, ƙaramar kuma Mikal.
The sons of Saul were Jonathan, Ishvi, and Malki-Shua. The names of his two daughters were Merab, the firstborn, and Michal, the younger.
50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam,’yar Ahimawaz. Sunan shugaban ƙungiyar sojan Shawulu kuwa Abner ne ɗan Ner, shi Ner kuwa ɗan’uwan mahaifin Shawulu ne.
The name of Saul's wife was Ahinoam; she was the daughter of Ahimaaz. The name of the captain of his army was Abner son of Ner, Saul's uncle.
51 Mahaifin Shawulu, Kish da kuma Ner mahaifin Abner,’ya’yan Abiyel ne.
Kish was Saul's father; and Ner, the father of Abner, was the son of Abiel.
52 Dukan kwanakin Shawulu sun kasance na yaƙe-yaƙe da Filistiyawa ne. Duk lokacin da Shawulu ya ga ƙaƙƙarfan mutum ko jarumi, sai yă ɗauke shi aikin sojansa.
There was hard fighting against the Philistines all the days of Saul. When Saul saw any mighty man, or any valiant man, he attached him to himself.

< 1 Sama’ila 14 >