< 1 Sarakuna 8 >

1 Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
Derpå kaldte Salomo Israels Ældste og alle Stammernes Overhoveder, Israeliternes Fædrenehuses Øverster, sammen hos sig i Jerusalem for at føre HERRENs Pagts Ark op fra Davidsbyen, det er Zion.
2 Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
Så samledes alle Israels Mænd hos Kong Salomo på Højtiden i Etanim Måned, det er den syvende Måned.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
Og alle Israels Ældste kom, og Præsterne bar Arken.
4 suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
Og de bragte HERRENs Ark op tillige med Åbenbaringsteltet og alle de hellige Ting, der var i Teltet; Præsterne og Leviterne bragte dem op.
5 sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
Og Kong Salomo tillige med hele Israels Menighed, som havde givet Møde hos ham foran Arken, ofrede Småkvæg og Hornkvæg, så meget, at det ikke var til at tælle eller overse.
6 Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
Så førte Præsterne HERRENs Pagts Ark ind på dens Plads i Templets Inderhal, det Allerhelligste, og stillede den under Kerubernes Vinger;
7 Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
thi Keruberne udbredte deres Vinger over Pladsen, hvor Arken stod, og således dannede Keruberne et Dække over Arken og dens Bærestænger.
8 Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
Stængerne var så lange, at Enderne af dem kunde ses fra det Hellige foran Inderhallen, men de kunde ikke ses længere ude; og de er der den Dag i Dag.
9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
Der var ikke andet i Arken end de to Stentavler, Moses havde lagt ned i den på Horeb, Tavlerne med den Pagt, HERREN havde sluttet med Israeliterne, da de drog bort fra Ægypten.
10 Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
Da Præsterne derpå gik ud af Helligdommen, fyldte Skyen HERRENs Hus,
11 Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
så at Præsterne af Skyen hindredes i at stå og udføre deres Tjeneste; thi HERRENs Herlighed fyldte HERRENs Hus.
12 Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
Ved den Lejlighed sang Salomo: HERREN satte Solen på Himlen, men selv, har han sagt, vil han bo i Mulmet.
13 ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
Nu har jeg bygget dig et Hus til Bolig, et Sted, du for evigt kan dvæle. Det står jo optegnet i Sangenes Bog.
14 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Derpå vendte Kongen sig om og velsignede hele Israels Forsamling, der imens stod op;
15 Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
og han sagde: "Lovet være HERREN, Israels Gud, hvis Hånd har fuldført, hvad hans Mund talede til min Fader David, dengang han sagde:
16 ‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Fra den Dag jeg førte mit Folk Israel ud af Ægypten, har jeg ikke udvalgt nogen By i nogen af Israels Stammer for der at bygge et Hus til Bolig for mit Navn; men Jerusalem udvalgte jeg til Bolig for mit Navn, og David udvalgte jeg til at herske over mit Folk Israel.
17 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Og min Fader David fik i Sinde at bygge HERRENs, Israels Guds, Navn et Hus;
18 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
men HERREN sagde til min Fader David: At du har i Sinde at bygge mit Navn et Hus, er ret af dig;
19 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
dog skal du ikke bygge det Hus, men din Søn, der udgår af din Lænd; skal bygge mit Navn det Hus.
20 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Nu har HERREN opfyldt det Ord, han talede, og jeg er trådt i min Fader Davids Sted og sidder på Israels Trone, som HERREN sagde, og jeg har bygget HERRENs, Israels Guds, Navn Huset;
21 Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
og jeg har der beredt en Plads til Arken med den Pagt, HERREN sluttede med vore Fædre, da han førte dem bort fra Ægypten."
22 Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
Derpå trådte Salomo frem foran HERRENs Alter lige over for hele Israels Forsamling, udbredte sine Hænder mod Himmelen
23 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
og sagde: "HERRE Israels Gud, der er ingen Gud som du i Himmelen oventil og på Jorden nedentil, du, som holder fast ved din Pagt og din Miskundhed mod dine Tjenere, når de af hele deres Hjerte vandrer for dit Åsyn,
24 Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
du, som har holdt, hvad du lovede din Tjener, min Fader David, og i Dag opfyldt med din Hånd, hvad du talede med din Mund.
25 “Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
Så hold da nu, HERRE, Israels Gud, hvad du lovede din Tjener, min Fader David, da du sagde: En Efterfølger skal aldrig fattes dig til at sidde på Israels Trone for mit Åsyn, når kun dine Sønner vil tage Vare på deres Vej og vandre for mit Åsyn, som du har gjort.
26 Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
Så lad nu, HERRE, Israels Gud, det Ord opfyldes, som du tilsagde din Tjener, min Fader David!
27 “Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
Men kan Gud da virkelig bo på Jorden? Nej visselig, Himlene, ja Himlenes Himle kan ikke rumme dig, langt mindre dette Hus, som jeg har bygget!
28 Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
Men vend dig til din Tjeners Bøn og Begæring, HERRE min Gud, så du hører det Råb og den Bøn, din Tjener i Dag opsender for dit Åsyn;
29 Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
lad dine Øjne være åbne over dette Hus både Nat og Dag, over det Sted, hvor du har sagt, dit Navn skal bo, så du hører den Bøn, din Tjener opsender, vendt mod dette Sted!
30 Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Og hør den Bøn, din Tjener og dit Folk Israel opsender, vendt mod dette Sted; du høre den der, hvor du bor, i Himmelen, du høre og tilgive!
31 “Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
Når nogen synder imod sin Næste, og man afkræver ham Ed og lader ham sværge, og han kommer og aflægger Ed foran dit Alter i dette Hus,
32 sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
så høre du det i Himmelen og gøre det og dømme dine Tjenere imellem, så du kender den skyldige skyldig og lader hans Gerning komme over hans Hoved og frikender den uskyldige og gør med ham efter hans Uskyld!
33 “Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
Når dit Folk Israel tvinges til at fly for en Fjende, fordi de synder imod dig, og de så omvender sig til dig og bekender dit Navn og opsender Bønner og Begæringer til dig i dette Hus,
34 ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
så høre du det i Himmelen og tilgive dit Folk Israels Synd og føre dem tilbage til det Land, du gav deres Fædre!
35 “Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
Når Himmelen lukkes, så Regnen udebliver, fordi de synder imod dig, og de så beder, vendt mod dette Sted, og bekender dit Navn og omvender sig fra deres Synd, fordi du revser dem,
36 ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
så høre du det i Himmelen og tilgive din Tjeners og dit Folk Israels Synd, ja du vise dem den gode Vej, de skal vandre, og lade det regne i dit Land, som du gav dit Folk i Eje!
37 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
Når der kommer Hungersnød i Landet, når der kommer Pest, når der kommer Kornbrand og Rust, Græshopper og Ædere, når Fjenden belejrer Folket i en af dets Byer, når alskens Plage og Sot indtræffer -
38 in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
enhver Bøn, enhver Begæring, hvem den end kommer fra i hele dit Folk Israel, når de føler sig truffet i deres Samvittighed og udbreder Hænderne mod dette Hus,
39 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
den høre du i Himmelen, der, hvor du bor, og tilgive og gøre det, idet du gengælder enhver hans Færd, fordi du kender hans Hjerte, thi du alene kender alle Menneskebørnenes Hjerter,
40 saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
for at de må frygte dig, al den Tid de lever på den Jord, du gav vore Fædre.
41 “Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
Selv den fremmede, der ikke hører til dit Folk Israel, men kommer fra et fjernt Land for dit Navns Skyld, -
42 gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
thi man vil høre om dit store Navn, din stærke Hånd og din udstrakte Arm - når han kommer og beder, vendt mod dette Hus,
43 ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
da høre du det i Himmelen, der, hvor du bor, og da gøre du efter alt, hvad den fremmede råber til dig om, for at alle Jordens Folkeslag må lære dit Navn at kende og frygte dig ligesom dit Folk Israel og erkende, at dit Navn er nævnet over dette Hus, som jeg har bygget.
44 “Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
Når dit Folk drager i Krig mod sin Fjende, hvor du end sender dem hen, og de beder til HERREN, vendt mod den By, du har udvalgt, og det Hus, jeg har bygget dit Navn,
45 ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
så høre du i Himmelen deres Bøn og Begæring og skaffe dem deres Ret!
46 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
Når de synder imod dig thi der er intet Menneske, som ikke synder - og du vredes på dem og giver dem i Fjendens Magt, og Sejrherrerne fører dem fangne til Fjendens Land, det være sig fjernt eller nær,
47 in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
og de så går i sig selv i det Land, de er bortført til, og omvender sig og råber til dig i Sejrherrernes Land og siger: Vi har syndet, handlet ilde og været ugudelige!
48 in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
når de omvender sig til dig af hele deres Hjerte og af hele deres Sjæl i deres Fjenders Land, som de bortførtes til, og de beder til dig, vendt mod deres Land, som du gav deres fædre, mod den By, du har udvalgt, og det Hus, jeg har bygget dit Navn
49 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
så høre du i Himmelen, der, hvor du bor, deres Bøn og Begæring og skaffe dem deres Ret,
50 Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
og du tilgive dit Folk, hvad de syndede imod dig, alle de Overtrædelser, hvori de gjorde sig skyldige imod dig, og lade dem finde Barmhjertighed hos Sejrherrerne, så de forbarmer sig over dem;
51 Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
de er jo dit Folk og din Ejendom, som du førte ud af Ægypten, af Smelteovnen.
52 “Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
Lad dine Øjne være åbne for din Tjeners og dit Folk Israels Begæring, så du hører dem, hver Gang de råber til dig.
53 Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
Thi du har udskilt dem fra alle Jordens Folkeslag til at være din Ejendom, som du lovede ved din Tjener Moses, da du førte vore Fædre bort fra Ægypten, Herre, HERRE!"
54 Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
Da Salomo var færdig med hele denne Bøn og Begæring til HERREN rejste han sig fra Pladsen foran HERRENs Alter, hvor han havde ligget på Knæ med Hænderne udbredt mod Himmelen.
55 Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
Derpå trådte han frem og velsignede med høj Røst hele Israels Forsamling, idet han sagde:
56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
"Lovet være HERREN, der har givet sit Folk Israel Hvile, ganske som han talede, uden at et eneste Ord er faldet til Jorden af alle de herlige Forjættelser, han udtalte ved sin Tjener Moses.
57 Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
HERREN vor Gud være med os, som han var med vore Fædre, han forlade og forstøde os ikke,
58 Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
at vort Hjerte må drages til ham, så vi vandrer på alle hans Veje og holder hans Bud, Anordninger og Lovbud, som han pålagde vøre Fædre!
59 Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
Måtte disse Bønner, som jeg har opsendt for HERRENs Åsyn, være nærværende for HERREN vor Gud både Nat og Dag, så han skaffer sin Tjener og sit Folk Israel Ret efter hver Dags Behov,
60 saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
for at alle Jordens Folk må kende, at HERREN og ingen anden er Gud.
61 Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
Og måtte eders Hjerte være helt med HERREN vor Gud, så I følger hans Anordninger og holder hans Bud som i Dag!"
62 Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Kongen ofrede nu sammen med hele Israel Slagtofre for HERRENs Åsyn.
63 Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
Til de Takofre, Salomo ofrede til HERREN, tog han 22 000 Stykker Hornkvæg og 12 000 Stykker Småkvæg. Således indviede Kongen og alle Israeliterne HERRNs Hus.
64 A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
Samme Dag helligede Kongen den mellemste Del af Forgården foran HERRENs Hus, thi der måtte han ofre Brændofrene, Afgrødeofrene og Fedtstykkerne af Takofrene, da Kobberalteret foran HERRENs Åsyn var for lille til at rumme Ofrene.
65 Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
Samtidig fejrede Salomo i syv Dage Højtiden for HERREN vor Guds Åsyn sammen med hele Israel, en vældig Forsamling (lige fra Egnen ved Hamat og til Ægyptens Bæk).
66 A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.
Ottendedagen lod han Folket gå, og de velsignede Kongen og drog hver til sit, glade og vel til Mode over al den Godhed, HERREN havde vist sin Tjener David og sit Folk Israel.

< 1 Sarakuna 8 >