< 1 Sarakuna 2 >

1 Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
Torej Davidovi dnevi so se približali, da naj bi umrl in svojemu sinu Salomonu je naročil, rekoč:
2 “Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
»Jaz grem pot vse zemlje. Bodi torej močan in se izkaži moža
3 ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
in ohrani naročilo Gospoda, svojega Boga, da hodiš po njegovih poteh, da ohranjaš njegove zakone, njegove zapovedi, njegove sodbe in njegova pričevanja, kakor je zapisano v Mojzesovi postavi, da boš lahko uspeval v vsem, kar delaš in kamorkoli se obrneš,
4 Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
da bo Gospod lahko nadaljeval svojo besedo, ki jo je govoril glede mene, rekoč: ›Če tvoji otroci pazijo na svojo pot, da hodijo pred menoj v resnici, z vsem svojim srcem in z vso svojo dušo, tebi ne bo odrezan, ‹ je rekel, ›noben mož na Izraelovem prestolu.‹
5 “Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
Poleg tega tudi veš, kaj mi je storil Cerújin sin Joáb in kaj je storil dvema poveljnikoma Izraelove vojske, Nerovemu sinu Abnêrju in Jeterjevemu sinu Amasáju, ki ju je ubil in vojno kri prelil v miru in vojno kri položil na svoj pas, ki je bil okrog njegovih ledij in na njegove čevlje, ki so bili na njegovih stopalih.
6 Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
Stori torej glede na svojo modrost in ne dopusti, da bi njegova osivela glava šla v miru dol v podzemlje. (Sheol h7585)
7 “Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
Toda izkazuj prijaznost sinovom Gileádca Barzilája in naj bodo izmed tistih, ki jedo pri tvoji mizi, kajti tako so prišli k meni, ko sem pobegnil zaradi tvojega brata Absaloma.
8 “Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
Glej, s seboj imaš Šimíja, Gerájevega sina, Benjaminovca iz Bahuríma, ki me je preklinjal z bolečim prekletstvom na dan, ko sem odšel v Mahanájim, toda prišel je dol, da me sreča pri Jordanu in prisegel sem mu pri Gospodu, rekoč: ›Ne bom te usmrtil z mečem.‹
9 Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
Zdaj ga torej ne imej brez krivde, kajti moder človek si in veš, kaj mu moraš storiti, temveč njegovo osivelo glavo s krvjo privedi dol k podzemlju.« (Sheol h7585)
10 Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
Tako je David zaspal s svojimi očeti in bil pokopan v Davidovem mestu.
11 Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
Dni, ko je David kraljeval nad Izraelom, je bilo štirideset let. Sedem let je kraljeval v Hebrónu, triintrideset let pa je kraljeval v Jeruzalemu.
12 Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
Potem se je Salomon usedel na prestol svojega očeta Davida in njegovo kraljestvo je bilo silno utrjeno.
13 To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
Hagítin sin Adoníja je prišel k Salomonovi materi Batšébi. Rekla je: »Prihajaš miroljubno?« Rekel je: »Miroljubno.«
14 Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
Poleg tega je rekel: »Nekaj ti imam povedati.« Rekla je: »Povej.«
15 Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
Rekel je: »Veš, da je bilo kraljestvo moje in da je ves Izrael svoje obraze naravnal name, da naj bi jaz kraljeval, vendar se je kraljestvo zaobrnilo in postalo bratovo, kajti njegovo je bilo od Gospoda.
16 Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
Sedaj od tebe prosim eno prošnjo, ne zavrni me.« Rekla mu je: »Povej.«
17 Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
Rekel je: »Spregovori, prosim te, kralju Salomonu (kajti ne bo ti rekel ne), da mi da za ženo Šunémko Abišágo.«
18 Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
Batšéba je rekla: »Dobro, zate bom govorila kralju.«
19 Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
Batšéba je torej šla h kralju Salomonu, da mu govori za Adoníja. Kralj je vstal, da jo sreča in se ji priklonil, se usedel na svoj prestol in dal postaviti sedež za kraljevo mater in usedla se je na njegovo desnico.
20 Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
Potem je rekla: »Od tebe želim eno majhno prošnjo, prosim te, ne reci mi ne.« Kralj ji je rekel: »Vprašaj, moja mati, kajti jaz ti ne bom rekel ne.«
21 Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
Rekla je: »Naj bo Šunémka Abišága dana tvojemu bratu Adoníju za ženo.«
22 Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
Kralj Salomon je odgovoril svoji materi in rekel: »Zakaj prosiš za Adoníja Šunémko Abišágo? Prosi zanj tudi kraljestvo, kajti on je moj starejši brat; celo zanj in za duhovnika Abjatárja in za Cerújinega sina Joába.«
23 Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
Potem je kralj Salomon prisegel pri Gospodu, rekoč: »Bog naj mi tako stori in še več, če ni Adoníja te besede spregovoril zoper svoje lastno življenje.
24 Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
Zdaj torej kakor živi Gospod, ki me je utrdil in me postavil na prestol mojega očeta Davida in ki mi je naredil hišo, kakor je obljubil, bo ta dan Adoníja usmrčen.«
25 Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
Kralj Salomon je poslal po roko Jojadájevega sina Benajá in ta je padel nanj, da je umrl.
26 Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
Duhovniku Abjatárju pa je kralj rekel: »Pojdi v Anatót, k svojim lastnim poljem, kajti vreden si smrti, toda tokrat te ne bom usmrtil, ker pred mojim očetom Davidom nosiš skrinjo Gospoda Boga in ker si bil prizadet v vsem, s čimer je bil prizadet moj oče.«
27 Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
Tako je Salomon vrgel ven Abjatárja, da ne bi bil duhovnik Gospodu, da je lahko izpolnil Gospodovo besedo, ki jo je govoril glede Élijeve hiše v Šilu.
28 Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
Potem so do Joába prišle novice, kajti Joáb se je obrnil za Adoníjem, čeprav se ni obrnil za Absalomom. Joáb je pobegnil h Gospodovemu šotorskemu svetišču in se oprijel oltarnih rogov.
29 Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
To je bilo povedano kralju Salomonu, da je Joáb pobegnil v Gospodovo šotorsko svetišče in glej, pri oltarju je. Potem je Salomon poslal Jojadájevega sina Benajá, rekoč: »Pojdi, padi nanj.«
30 Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
Benajá je prišel v Gospodovo šotorsko svetišče ter mu rekel: »Tako govori kralj: ›Pridi naprej.‹« Rekel je: »Ne, temveč bom tukaj umrl.« Benajá je kralju ponovno prinesel besedo, rekoč: »Tako je rekel Joáb in tako mi je odgovoril.«
31 Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
Kralj mu je rekel: »Stôri, kakor je rekel, padi nanj in ga pokoplji, da boš lahko od mene in od hiše mojega očeta odvzel nedolžno kri, ki jo je prelil Joáb.
32 Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
Gospod bo njegovo kri povrnil na njegovo lastno glavo, ker je padel na dva moža, pravičnejša in boljša kakor on in ju umoril z mečem, moj oče David pa ni vedel o tem, namreč Nerovega sina Abnêrja, poveljnika Izraelove vojske in Jeterjevega sina Amasája, poveljnika Judove vojske.
33 Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
Njuna kri se bo torej povrnila na Joábovo glavo in na glavo njegovega semena na veke, toda nad Davidom, nad njegovim semenom, nad njegovo hišo in nad njegovim prestolom bo mir na veke od Gospoda.«
34 Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
Tako je Jojadájev sin Benajá odšel gor, padel nanj, ga usmrtil in pokopan je bil v svoji lastni hiši v divjini.
35 Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
Na njegovo mesto, čez vojsko, je kralj postavil Jojadájevega sina Benajá, na Abjatárjevo mesto pa je kralj postavil duhovnika Cadóka.
36 Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
Kralj je poslal in poklical Šimíja ter mu rekel: »Zgradi si hišo v Jeruzalemu in tam prebivaj in ne hodi kamorkoli od tam.
37 Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
Kajti tako bo, da na dan, ko pojdeš ven in preideš potok Kidron, boš zagotovo vedel, da boš zagotovo umrl. Tvoja kri bo na tvoji lastni glavi.«
38 Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
Šimí je rekel kralju: »Ta beseda je dobra, kakor je rekel moj gospod kralj, tako bo tvoj služabnik storil.« In Šimí je mnogo dni prebival v Jeruzalemu.
39 Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
Pripetilo pa se je ob koncu treh let, da sta dva izmed Šimíjevih služabnikov pobegnila k Maahájevemu sinu Ahíšu, kralju iz Gata. Šimíju so povedali, rekoč: »Glej, tvoja služabnika sta v Gatu.«
40 Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
Šimí je vstal, osedlal svojega osla in šel v Gat, k Ahíšu, da poišče svoja služabnika. Šimí je odšel in svoja služabnika privedel iz Gata.
41 Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
To je bilo povedano Salomonu, da je Šimí iz Jeruzalema odšel v Gat in ponovno prišel nazaj.
42 Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
Kralj je poslal in dal poklicati Šimíja ter mu rekel: »Mar te nisem primoral, da prisežeš pri Gospodu in ti izpričal, rekoč: ›Zagotovo vedi, na dan, ko greš ven in hodiš kakorkoli naokoli, da boš zagotovo umrl?‹ In rekel si mi: ›Beseda, ki sem jo slišal, je dobra.‹
43 To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
Zakaj se potem nisi držal Gospodove prisege in zapovedi, ki sem ti jo naročil?«
44 Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
Kralj je poleg tega Šimíju rekel: »Ti poznaš vso zlobnost, ki je znana tvojemu srcu, ki si jo storil mojemu očetu Davidu, zato bo Gospod tvojo zlobnost povrnil na tvojo lastno glavo
45 Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
in kralj Salomon bo blagoslovljen in Davidov prestol bo pred Gospodom utrjen na veke.«
46 Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.
Tako je kralj zapovedal Jojadájevemu sinu Benajáju, ki je odšel ven in padel nanj, da je ta umrl. In kraljestvo je bilo utrjeno v Salomonovi roki.

< 1 Sarakuna 2 >