< 1 Sarakuna 12 >

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
Et Roboam alla à Sichem, car tout Israël était venu à Sichem pour le faire roi.
2 Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
Et quand Jéroboam, fils de Nebath, l’apprit (il était encore en Égypte, où il s’était enfui de devant le roi Salomon, et Jéroboam habitait l’Égypte;
3 Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
et ils envoyèrent et l’appelèrent), il arriva que Jéroboam et toute la congrégation d’Israël vinrent et parlèrent à Roboam, disant:
4 “Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Ton père a rendu notre joug dur; et toi, maintenant, allège le dur service de ton père et son joug pesant qu’il a mis sur nous, et nous te servirons.
5 Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
Et il leur dit: Allez-vous-en encore pour trois jours, et revenez vers moi. Et le peuple s’en alla.
6 Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
Et le roi Roboam tint conseil avec les vieillards qui s’étaient tenus devant Salomon, son père, lorsqu’il vivait, disant: Comment conseillez-vous de répondre à ce peuple?
7 Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
Et ils lui parlèrent, disant: Si aujourd’hui tu deviens serviteur de ce peuple, et que tu les serves, et leur répondes, et leur dises de bonnes paroles, ils seront toujours tes serviteurs.
8 Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
Mais il laissa le conseil des vieillards, qu’ils lui avaient donné, et tint conseil avec les jeunes gens qui avaient grandi avec lui, qui se tenaient devant lui;
9 Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
et il leur dit: Que conseillez-vous que nous répondions à ce peuple, qui m’a parlé, disant: Allège le joug que ton père a mis sur nous?
10 Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
Et les jeunes gens qui avaient grandi avec lui, lui parlèrent, disant: Tu diras ainsi à ce peuple qui t’a parlé, disant: Ton père a rendu pesant notre joug; toi, allège-le de dessus nous; – tu leur diras ainsi: Mon petit doigt est plus gros que les reins de mon père;
11 Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
et maintenant, mon père a chargé sur vous un joug pesant, et moi j’ajouterai à votre joug; mon père vous a corrigés avec des fouets, et moi je vous corrigerai avec des scorpions.
12 Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
Et Jéroboam et tout le peuple vinrent vers Roboam le troisième jour, comme le roi avait dit, en disant: Revenez vers moi le troisième jour.
13 Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
Et le roi répondit au peuple avec dureté, et laissa le conseil que les vieillards lui avaient donné;
14 Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
et il leur parla selon le conseil des jeunes gens, disant: Mon père a rendu pesant votre joug, et moi j’ajouterai à votre joug; mon père vous a corrigés avec des fouets, et moi je vous corrigerai avec des scorpions.
15 Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
Et le roi n’écouta pas le peuple, car cela était amené par l’Éternel, afin d’accomplir sa parole, que l’Éternel avait dite par Akhija, le Silonite, à Jéroboam, fils de Nebath.
16 Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
Et tout Israël vit que le roi ne les avait pas écoutés. Et le peuple répondit au roi, disant: Quelle part avons-nous en David? Et nous n’avons pas d’héritage dans le fils d’Isaï. À tes tentes, Israël! Maintenant, David, regarde à ta maison! Et Israël s’en alla à ses tentes.
17 Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
Mais quant aux fils d’Israël qui habitaient dans les villes de Juda, Roboam régna sur eux.
18 Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
Et le roi Roboam envoya Adoram, qui était préposé sur les levées; et tout Israël le lapida avec des pierres, et il mourut. Et le roi Roboam se hâta de monter sur un char pour s’enfuir à Jérusalem.
19 Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
Et Israël se rebella contre la maison de David, jusqu’à ce jour.
20 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
Et il arriva que, quand tout Israël apprit que Jéroboam était de retour, ils envoyèrent et l’appelèrent à l’assemblée, et l’établirent roi sur tout Israël. Il n’y eut que la tribu de Juda seule qui suive la maison de David.
21 Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
Et Roboam s’en alla à Jérusalem. Et il assembla toute la maison de Juda, et la tribu de Benjamin, 180 000 hommes d’élite propres à la guerre, pour faire la guerre à la maison d’Israël, afin de ramener le royaume à Roboam, fils de Salomon.
22 Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
Et la parole de Dieu vint à Shemahia, homme de Dieu, disant:
23 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
Parle à Roboam, fils de Salomon, roi de Juda, et à toute la maison de Juda et de Benjamin, et au reste du peuple, disant:
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
Ainsi dit l’Éternel: Ne montez pas, et ne faites pas la guerre à vos frères, les fils d’Israël; retournez chacun à sa maison, car c’est de par moi que cette chose a eu lieu. Et ils écoutèrent la parole de l’Éternel, et s’en retournèrent pour s’en aller, selon la parole de l’Éternel.
25 Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
Et Jéroboam bâtit Sichem dans la montagne d’Éphraïm, et y habita; et il sortit de là, et bâtit Penuel.
26 Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
Et Jéroboam dit en son cœur: Maintenant le royaume retournera à la maison de David.
27 In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
Si ce peuple monte pour offrir des sacrifices dans la maison de l’Éternel à Jérusalem, le cœur de ce peuple retournera à son seigneur, à Roboam, roi de Juda, et ils me tueront, et ils retourneront à Roboam, roi de Juda.
28 Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
Et le roi prit conseil, et fit deux veaux d’or, et dit au peuple: C’est trop pour vous de monter à Jérusalem; voici tes dieux, Israël! qui t’ont fait monter du pays d’Égypte.
29 Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
Et il en mit un à Béthel, et l’autre il le plaça à Dan.
30 Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
Et cela devint un péché, et le peuple alla devant l’un [des veaux] jusqu’à Dan.
31 Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
Et il fit une maison de hauts lieux, et établit des sacrificateurs d’entre toutes les classes du peuple, lesquels n’étaient pas des fils de Lévi.
32 Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
Et Jéroboam établit une fête au huitième mois, le quinzième jour du mois, comme la fête qui [avait lieu] en Juda; et il offrit sur l’autel. Il fit ainsi à Béthel, sacrifiant aux veaux qu’il avait faits, et il plaça à Béthel les sacrificateurs des hauts lieux qu’il avait établis.
33 A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.
Et il offrit sur l’autel qu’il avait fait à Béthel, le quinzième jour du huitième mois, le mois qu’il avait imaginé dans son propre cœur; et il fit une fête pour les fils d’Israël, et offrit sur l’autel, faisant fumer l’encens.

< 1 Sarakuna 12 >