< 1 Sarakuna 1 >

1 Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
Now King David was old and far on in years; and though they put covers over him, his body was cold.
2 Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
So his servants said to him, Let search be made for a young virgin for my lord the king, to take care of him and be waiting on him; and you may take her in your arms, and so my lord the king will be warm.
3 Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
So after searching through all the land of Israel for a fair young girl, they saw Abishag the Shunammite, and took her to the king.
4 Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
Now she was very beautiful; and she took care of the king, waiting on him at all times; but the king had no connection with her.
5 Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
Then Adonijah, the son of Haggith, lifting himself up in pride, said, I will become king; and he made ready his carriages of war and his horsemen, with fifty runners to go before him.
6 (A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
Now all his life his father had never gone against him or said to him, Why have you done so? and he was a very good-looking man, and younger than Absalom.
7 Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
And he had talk with Joab, the son of Zeruiah, and with Abiathar the priest; and they were on his side and gave him their support.
8 Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
But Zadok the priest, and Benaiah, the son of Jehoiada, and Nathan the prophet and Shimei and Rei, and David's men of war did not take the side of Adonijah.
9 Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
Then Adonijah put to death sheep and oxen and fat beasts by the stone of Zoheleth, by En-rogel; and he sent for all his brothers, the king's sons, and all the men of Judah, the king's servants, to come to him:
10 amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
But he did not send for Nathan the prophet and Benaiah and the other men of war and Solomon his brother.
11 Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
Then Nathan said to Bath-sheba, the mother of Solomon, Has it not come to your ears that Adonijah, the son of Haggith, has made himself king without the knowledge of David our lord?
12 Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
So now, let me make a suggestion, so that you may keep your life safe and the life of your son Solomon.
13 Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
Come now, go to King David and say to him, Did you not, O my lord, take an oath to me, your servant, saying, Truly Solomon your son will be king after me, seated on the seat of my kingdom? why then is Adonijah acting as king?
14 Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
And while you are still talking there with the king, see, I will come in after you and say that your story is true.
15 Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
Then Bath-sheba went into the king's room; now the king was very old, and Abishag the Shunammite was waiting on him.
16 Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
And Bath-sheba went down on her face on the earth before the king giving him honour. And he said, What is your desire?
17 Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
And she said to him, My lord, you took an oath by the Lord your God and gave your word to your servant, saying, Truly, Solomon your son will be king after me, seated on the seat of my kingdom.
18 Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
And now, see, Adonijah has made himself king without my lord's knowledge;
19 Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
And has put to death oxen and fat beasts and sheep in great numbers, and has sent for all the sons of the king, and Abiathar the priest, and Joab, the captain of the army; but he has not sent for Solomon your servant.
20 Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
And now, my lord the king, the eyes of all Israel are on you, waiting for you to say who is to take the place of my lord the king after him.
21 In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
For as things are, it will come about, when my lord the king is sleeping with his fathers, that I and Solomon my son will be made outlaws.
22 Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
And while she was still talking with the king, Nathan the prophet came in.
23 Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And they said to the king, Here is Nathan the prophet. And when he came in before the king, he went down on his face on the earth.
24 Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
And Nathan said, O my lord king, have you said, Adonijah is to be king after me, seated on the seat of my kingdom?
25 Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
Because today he has gone down and has put to death oxen and fat beasts and sheep in great numbers, and has sent for all the king's sons to come to him, with the captains of the army and Abiathar the priest; and they are feasting before him and crying, Long life to King Adonijah!
26 Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
But me, your servant, and Zadok the priest, and Benaiah, the son of Jehoiada, and your servant Solomon, he has not sent for.
27 Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
Has this thing been done by my lord the king, without giving word to your servants who was to be placed on my lord the king's seat after him?
28 Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
Then King David in answer said, Send for Bath-sheba to come to me. And she came in and took her place before the king.
29 Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
And the king took an oath, and said, By the living Lord, who has been my saviour from all my troubles,
30 tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
As I took an oath to you by the Lord, the God of Israel, saying, Certainly Solomon your son will become king after me, seated on my seat in my place; so will I do this day.
31 Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
Then Bath-sheba went down on her face on the earth before the king giving him honour, and said, May my lord King David go on living for ever.
32 Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
And King David said, Send for Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah, the son of Jehoiada. And they came before the king.
33 sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
And the king said to them, Take with you the servants of your lord, and put Solomon my son on my beast, yes, mine, and take him down to Gihon;
34 A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
And there let Zadok the priest and Nathan the prophet put the holy oil on him to make him king over Israel; and sounding the horn say, Long life to King Solomon!
35 Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
Then come up after him and he will come in and take his place on the seat of my kingdom; for he is to be king in my place, and I have given orders that he is to be ruler over Israel and over Judah.
36 Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
And Benaiah, the son of Jehoiada, answering the king, said, So be it: and may the Lord, the God of my lord the king, say so.
37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
As the Lord has been with my lord the king, even so may he be with Solomon and make the seat of his authority greater than that of my lord King David.
38 Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
So Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah, the son of Jehoiada, and the Cherethites and the Pelethites, went down and put Solomon on King David's beast and took him to Gihon.
39 Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
And Zadok the priest took the vessel of oil out of the Tent, and put the holy oil on Solomon. And when the horn was sounded, all the people said, Long life to King Solomon!
40 Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
And all the people came up after him, piping with pipes, and they were glad with great joy, so that the earth was shaking with the sound.
41 Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
And it came to the ears of Adonijah and all the guests who were with him, when their meal was ended. And Joab, hearing the sound of the horn, said, What is the reason of this noise as if the town was worked up?
42 Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
And while the words were on his lips, Jonathan, the son of Abiathar the priest, came; and Adonijah said, Come in; for you are a man of good faith and the news which you have for us will be good.
43 Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
And Jonathan, answering, said to Adonijah, Not so, but our lord King David has made Solomon king:
44 Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
And he sent with him Zadok the priest, and Nathan the prophet, and Benaiah, the son of Jehoiada, and the Cherethites and the Pelethites; and they put him on the king's beast:
45 Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
And Zadok the priest and Nathan the prophet put the holy oil on him and made him king in Gihon; and they came back from there with joy, and the town was all worked up. This is the noise which has come to your ears.
46 Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
And now Solomon is seated on the seat of the kingdom.
47 Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
And the king's servants came to our lord King David, blessing him and saying, May God make the name of Solomon better than your name, and the seat of his authority greater than your seat; and the king was bent low in worship on his bed.
48 ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
Then the king said, May the God of Israel be praised, who has given one of my seed to be king in my place this day and has let my eyes see it.
49 A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
And all the guests of Adonijah got up in fear and went away, every man to his place.
50 Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
And Adonijah himself was full of fear because of Solomon; and he got up and went to the altar, and put his hands on its horns.
51 Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
And they gave Solomon word of it, saying, See, Adonijah goes in such fear of King Solomon, that he has put his hands on the horns of the altar, saying, Let King Solomon first give me his oath that he will not put his servant to death with the sword.
52 Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
And Solomon said, If he is seen to be a man of good faith, not a hair of him will be touched; but if any wrongdoing is seen in him, he is to be put to death.
53 Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”
So King Solomon sent, and they took him down from the altar. And he came and gave honour to King Solomon; and Solomon said to him, Go to your house.

< 1 Sarakuna 1 >