< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
The work groups based on Aaron's descendants were these: Nadab, Abihu, Eleazar and Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
Nadab and Abihu died before their father died. They had no children, so Eleazar and Ithamar served as priests.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
David, together with Zadok, a descendant of Eleazar, and Ahimelech, a descendant of Ithamar, divided them into groups for their work as priests.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
There were more leading men among Eleazar's descendants than among Ithamar's descendants, so they divided Eleazar's descendants into sixteen groups. They did this by heads of clans and by Ithamar's descendants. These divisions were eight in number, corresponding to their clans.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
They divided them impartially by lot, for there were holy officials and officials of God, from both Eleazar's descendants and Ithamar's descendants.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Shemaiah son of Nethanel the scribe, a Levite, wrote down their names in the presence of the king, the officials, Zadok the priest, Ahimelech son of Abiathar, and the leaders of the priestly and Levite families. One clan was drawn by lot from Eleazar's descendants, and then the next would be drawn from Ithamar's descendants.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
The first lot went to Jehoiarib, the second to Jedaiah,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
the third to Harim, the fourth to Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
the fifth to Malchijah, the sixth to Mijamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
the seventh to Hakkoz, the eighth to Abijah,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
the ninth to Jeshua, the tenth to Shecaniah,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
the eleventh to Eliashib, the twelfth to Jakim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
the thirteenth to Huppah, the fourteenth to Jeshebeab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
the fifteenth to Bilgah, the sixteenth to Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
the seventeenth to Hezir, the eighteenth to Happizzez,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
the nineteenth to Pethahiah, the twentieth to Jehezkel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
the twenty-first to Jakin, the twenty-second to Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
the twenty-third to Delaiah, and the twenty-fourth to Maaziah.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
This was the order of their service, when they came into Yahweh's house, following the procedure given to them by Aaron their ancestor, as Yahweh, the God of Israel, had instructed him.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
These were the rest of the descendants of Levi: Of the sons of Amram, Shubael; of the sons of Shubael, Jehdeiah.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
As for Rehabiah, the sons of Rehabiah: Ishijah the leader.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
From the Izharites: Shelomoth; from the sons of Shelomoth: Jahath.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
The sons of Hebron: Jeriah the leader, Amariah the second, Jahaziel the third, and Jekameam the fourth.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
The son of Uzziel: Micah; from the sons of Micah: Shamir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
The brother of Micah: Ishijah. From the sons of Ishijah: Zechariah.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
The sons of Merari: Mahli and Mushi; from the son of Jaaziah: Beno.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
The sons of Merari from Jaaziah: Beno, Shoham, Zaccur, and Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
From Mahli: Eleazar, who had no sons.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
From Kish: The son of Kish: Jerahmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
The sons of Mushi: Mahli, Eder, and Jerimoth. These were the Levites, listed by their families.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
These men who were the head of each father's house and each of their younger brothers, cast lots in the presence of King David, and Zadok and Ahimelech, along with the leaders of the families of the priests and Levites. They cast lots just as Aaron's descendants had done.

< 1 Tarihi 24 >