< 1 Tarihi 23 >

1 Sa’ad da Dawuda ya tsufa yana kuma da cikakken shekaru, ya sa ɗansa Solomon sarki bisa Isra’ila.
So when David was old and full of days, he made Solomon his son king over Israel.
2 Ya kuma tattara dukan shugabannin Isra’ila a wuri ɗaya, haka kuma ya yi da firistoci da Lawiyawa.
And he assembled all the princes of Israel, with the priests and the Levites.
3 Aka ƙidaya Lawiyawan da suke’yan shekaru talatin da haihuwa ko fiye, suka kai wajen mutum dubu talatin da takwas.
Now the Levites were numbered from the age of thirty years and upward: and their number by their polls, man by man, was thirty and eight thousand.
4 Dawuda ya ce, “Cikin waɗannan, dubu ashirin da huɗu za su lura da aikin haikalin Ubangiji, dubu shida su zama manyan na ma’aikata da alƙalai.
Of which, twenty and four thousand [were] to oversee the work of the house of the LORD; and six thousand [were] officers and judges:
5 Dubu huɗu su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu kuma su yabi Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda na tanada saboda wannan manufa.”
Moreover, four thousand [were] porters; and four thousand praised the LORD with the instruments which I made, [said David], to praise [with them].
6 Dawuda ya rarraba Lawiyawa ƙungiya-ƙungiya bisa ga’ya’yan Lawi maza. Gershon, Kohat da Merari.
And David divided them into courses among the sons of Levi, [namely], Gershon, Kohath, and Merari.
7 Na Gershonawa, Ladan da Shimeyi.
Of the Gershonites, [were], Laadan and Shimei.
8 ’Ya’yan Ladan maza su ne, Yehiyel na farko, Zetam da Yowel, su uku ne duka.
The sons of Laadan: the chief [was] Jehiel, and Zetham, and Joel, three.
9 ’Ya’yan Shimeyi maza su ne, Shelomot, Haziyel da Haran, su uku ne duka. Waɗannan su ne kawunan iyalan Ladan.
The sons of Shimei; Shelomith, and Haziel, and Haran, three. These [were] the chief of the fathers of Laadan.
10 ’Ya’yan Shimeyi maza kuwa su ne, Yahat, Zina, Yewush da Beriya. Waɗannan su ne’ya’yan Shimeyi maza, su huɗu ne duka.
And the sons of Shimei [were], Jahath, Zina, and Jeush and Beriah. These four [were] the sons of Shimei.
11 Yahat shi ne na fari, Ziza kuma na biyu, amma Yewush da Beriya ba su haifi’ya’ya maza da yawa ba; saboda haka aka ƙidaya su kamar iyali ɗaya a wurin rabon aiki.
And Jahath was the chief, and Zizah the second: but Jeush and Beriah had not many sons; therefore they were in one reckoning, according to [their] father's house.
12 ’Ya’yan Kohat maza su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel, su huɗu ne duka.
The sons of Kohath; Amram, Izhar, Hebron, and Uzziel, four.
13 ’Ya’yan Amram maza su ne, Haruna da Musa. Haruna shi ne aka keɓe, shi da zuriyarsa har abada, don su tsarkake kayayyakin mafi tsarki, su miƙa hadayu a gaban Ubangiji, su yi hidima a gabansa su kuma furta albarku a cikin sunansa har abada.
The sons of Amram; Aaron and Moses: and Aaron was separated, that he should sanctify the most holy things, he and his sons for ever, to burn incense before the LORD, to minister to him, and to bless in his name for ever.
14 An ƙidaya aka kuma haɗa’ya’yan Musa maza mutumin Allah a sashen kabilar Lawi.
Now [concerning] Moses the man of God, his sons were named of the tribe of Levi.
15 ’Ya’yan Musa maza su ne, Gershom da Eliyezer.
The sons of Moses [were], Gershom, and Eliezer.
16 Zuriyar Gershom su ne, Shebuwel ne ɗan fari.
Of the sons of Gershom; Shebuel [was] the chief.
17 Zuriyar Eliyezer su ne, Rehabiya ne ɗan fari. Eliyezer ba shi da waɗansu’ya’ya maza, amma’ya’yan Rehabiya maza sun yi yawa.
And the sons of Eliezer [were], Rehabiah the chief. And Eliezer had no other sons; but the sons of Rehabiah were very many.
18 ’Ya’yan Izhar maza su ne, Shelomit ne ɗan fari.
Of the sons of Izhar; Shelomith the chief.
19 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
Of the sons of Hebron; Jeriah the first, Amariah the second, Jehaziel the third, and Jekameam the fourth.
20 ’Ya’yan Uzziyel maza su ne, Mika na fari da Isshiya na biyu.
Of the sons of Uzziel; Micah the first, and Jesiah the second.
21 ’Ya’yan Merari maza su ne, Mali da Mushi.’Ya’yan Mali maza su ne, Eleyazar da Kish.
The sons of Merari; Mahli, and Mushi. The sons of Mahli; Eleazar, and Kish.
22 Eleyazar ya mutu ba’ya’yan maza, yana da’ya’ya mata ne kawai.’Yan’uwansu,’ya’yan Kish maza, suka aure su.
And Eleazar died, and had no sons, but daughters: and their brethren the sons of Kish took them.
23 ’Ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yeremot, su uku ne duka.
The sons of Mushi; Mahli, and Eder, and Jeremoth, three.
24 Waɗannan ne zuriyar Lawi bisa ga iyalansu, kawunan iyalai kamar yadda aka rubuta su a ƙarƙashin sunayensu aka kuma ƙirga kowa, wato, masu aikin da suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye waɗanda suka yi hidima a cikin haikalin Ubangiji.
These [were] the sons of Levi after the house of their fathers; [even] the chief of the fathers, as they were counted by number of names by their polls, that did the work for the service of the house of the LORD, from the age of twenty years and upward.
25 Gama Dawuda ya ce, “Tun da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da hutu ga mutanensa, ya kuma zo ya zauna a Urushalima har abada,
For David said, The LORD God of Israel hath given rest to his people, that they may dwell in Jerusalem for ever;
26 Lawiyawa ba sa ƙara bukata su ɗauki tabanakul ko kuwa waɗansu kayayyakin da ake amfani da su a hidima.”
And also to the Levites: they shall no [more] carry the tabernacle, nor any vessels of it for its service.
27 Bisa ga umarnin ƙarshe na Dawuda, za a ƙidaya Lawiyawa daga’yan shekara ashirin ko fiye.
For by the last words of David the Levites [were] numbered from twenty years old and above:
28 Aikin Lawiyawa shi ne su taimaki zuriyar Haruna a hidimar haikalin Ubangiji; su lura da filaye da kuma ɗakunan da suke gefe, su tsarkake dukan kayayyaki masu tsarki, su kuma yi waɗansu ayyuka a gidan Allah.
Because their office [was] to wait on the sons of Aaron for the service of the house of the LORD, in the courts, and in the chambers, and in the purifying of all holy things, and the work of the service of the house of God;
29 Su ne za su lura da burodin da aka ajiye a tebur, lallausan gari don hadaya ta gari, waina marar yisti, toyawa da kwaɓawa, da kuma dukan awon yawa da kuma girman abubuwa.
Both for the show-bread, and for the fine flour for meat-offering, and for the unleavened cakes, and for [that which is baked in] the pan, and for that which is fried, and for all manner of measure and size;
30 Su ne kuma za su tsaya kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Za su kuma yi haka da yamma
And to stand every morning to thank and praise the LORD, and likewise at evening;
31 da kuma a duk sa’ad da aka miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a Asabbatai da bukukkuwan Sabon Wata da kuma a ƙayyadaddun bukukkuwa, za su yi hidima a gaban Ubangiji kullum bisa ga yawan da aka tsara da kuma a hanyar da aka tsara musu.
And to offer all burnt-sacrifices to the LORD on the sabbaths, in the new moons, and on the set feasts, by number, according to the order commanded to them, continually before the LORD:
32 A haka kuwa Lawiyawa suka yi ayyukansu don Tentin Sujada, don Wuri Mai Tsarki da kuma a ƙarƙashin’yan’uwansu zuriyar Haruna, saboda hidimar haikalin Ubangiji.
And that they should keep the charge of the tabernacle of the congregation, and the charge of the holy [place], and the charge of the sons of Aaron their brethren, in the service of the house of the LORD.

< 1 Tarihi 23 >