< 1 Tarihi 21 >

1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
And there standeth up an adversary against Israel, and persuadeth David to number Israel,
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
And David saith unto Joab, and unto the heads of the people, 'Go, number Israel from Beer-Sheba even unto Dan, and bring unto me, and I know their number.'
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
And Joab saith, 'Jehovah doth add to His people as they are a hundred times; are they not, my lord, O king, all of them to my lord for servants? why doth my lord seek this? why is he for a cause of guilt to Israel?'
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
And the word of the king [is] severe against Joab, and Joab goeth out, and goeth up and down in all Israel, and cometh in to Jerusalem.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
And Joab giveth the account of the numbering of the people unto David, and all Israel is a thousand thousand and a hundred thousand, each drawing sword, and Judah [is] four hundred and seventy thousand, each drawing sword.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
And Levi and Benjamin he hath not numbered in their midst, for the word of the king was abominable with Joab.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
And it is evil in the eyes of God concerning this thing, and He smiteth Israel,
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
and David saith unto God, 'I have sinned exceedingly, in that I have done this thing; and now, cause to pass away, I pray Thee, the iniquity of Thy servant, for I have acted very foolishly.'
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
And Jehovah speaketh unto Gad, seer of David, saying:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’”
'Go, and thou hast spoken unto David, saying, Thus said Jehovah, Three — I am stretching out unto thee; choose for thee one of these, and I do [it] to thee.'
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
And Gad cometh in unto David, and saith to him, 'Thus said Jehovah, Take for thee —
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
either for three years — famine, or three months to be consumed from the face of thine adversaries, even the sword of thine enemies to overtake, or three days the sword of Jehovah, even pestilence in the land, and a messenger of Jehovah destroying in all the border of Israel; and now, see; what word do I return to Him who is sending me?'
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
And David saith unto Gad, 'I am greatly distressed, let me fall, I pray thee, into the hand of Jehovah, for very many [are] His mercies, and into the hand of man let me not fall.'
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
And Jehovah giveth a pestilence in Israel, and there fall of Israel seventy thousand men,
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
and God sendeth a messenger to Jerusalem to destroy it, and as he is destroying Jehovah hath seen, and is comforted concerning the evil, and saith to the messenger who [is] destroying, 'Enough, now, cease thy hand.' And the messenger of Jehovah is standing by the threshing-floor of Ornan the Jebusite,
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
and David lifteth up his eyes, and seeth the messenger of Jehovah standing between the earth and the heavens, and his sword drawn in his hand, stretched out over Jerusalem, and David falleth, and the elders, covered with sackcloth, on their faces.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
And David saith unto God, 'Did not I — I say to number the people? Yea, I it [is] who have sinned, and done great evil: and these, the flock, what did they? O Jehovah, my God, let, I pray Thee, Thy hand be on me, and on the house of my father, and not on Thy people — to be plagued.'
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
And the messenger of Jehovah spake unto Gad, saying for David, 'Surely David doth go up to raise an altar to Jehovah in the threshing-floor of Ornan the Jebusite.'
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
And David goeth up by the word of Gad, that he spake in the name of Jehovah.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika;’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
And Ornan turneth back, and seeth the messenger, and his four sons [are] with him, hiding themselves, and Ornan is threshing wheat.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
And David cometh in unto Ornan, and Ornan looketh attentively, and seeth David, and goeth out from the threshing-floor, and boweth himself to David — face to the earth.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
And David saith unto Ornan, 'Give to me the place of the threshing-floor, and I build in it an altar to Jehovah; for full silver give it to me, and the plague is restrained from the people.'
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
And Ornan saith unto David, 'Take to thee — and my lord the king doth that which is good in his eyes: see, I have given the oxen for burnt-offerings, and the threshing instruments for wood, and the wheat for a present; the whole I have given.'
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
And king David saith to Ornan, 'Nay, for I surely buy for full silver; for I do not lift up that which is thine to Jehovah, so as to offer a burnt-offering without cost.'
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
And David giveth to Ornan for the place shekels of gold [in] weight six hundred;
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
and David buildeth there an altar to Jehovah, and offereth burnt-offerings and peace-offerings, and calleth unto Jehovah, and He answereth him with fire from the heavens on the altar of the burnt-offering.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
And Jehovah saith to the messenger, and he turneth back his sword unto its sheath.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
At that time when David seeth that Jehovah hath answered him in the threshing-floor of Ornan the Jebusite, then he sacrificeth there;
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
and the tabernacle of Jehovah that Moses made in the wilderness, and the altar of the burnt-offering, [are] at that time in a high place, in Gibeon;
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
and David is not able to go before it to seek God, for he hath been afraid because of the sword of the messenger of Jehovah.

< 1 Tarihi 21 >