< 1 Tarihi 15 >

1 Bayan Dawuda ya yi gine-gine wa kansa a Birnin Dawuda, sai ya shirya wuri domin akwatin alkawarin Allah, ya kuma kafa tenti dominsa.
And [David] made him houses in the city of David, and prepared a place for the ark of God, and pitched for it a tent.
2 Sa’an nan Dawuda ya ce, “Babu wani sai ko Lawiyawa kaɗai za su ɗauka akwatin alkawarin Allah, gama Ubangiji ya zaɓe su su ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji su kuma yi hidima a gabansa har abada.”
Then David said, None ought to carry the ark of God but the Levites: for them hath the LORD chosen to carry the ark of God, and to minister to him for ever.
3 Dawuda ya tattara dukan Isra’ila a Urushalima don su haura da akwatin alkawarin Ubangiji zuwa wurin da aka shirya dominsa.
And David assembled all Israel to Jerusalem, to bring up the ark of the LORD to its place, which he had prepared for it.
4 Ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya da kuma Lawiyawa.
And David assembled the children of Aaron, and the Levites:
5 Daga zuriyar Kohat, Uriyel shugaba da dangi 120;
Of the sons of Kohath; Uriel the chief, and his brethren a hundred and twenty:
6 daga zuriyar Merari Asahiya shugaba da dangi 220;
Of the sons of Merari; Asaiah the chief, and his brethren two hundred and twenty:
7 daga zuriyar Gershom, Yowel shugaba da dangi 130;
Of the sons of Gershom; Joel the chief, and his brethren a hundred and thirty:
8 daga zuriyar Elizafan, Shemahiya shugaba da dangi 200;
Of the sons of Elizaphan; Shemaiah the chief, and his brethren two hundred:
9 daga zuriyar Hebron, Eliyel shugaba da dangi 80;
Of the sons of Hebron; Eliel the chief, and his brethren eighty:
10 daga zuriyar Uzziyel, Amminadab shugaba da dangi 112.
Of the sons of Uzziel: Amminadab the chief, and his brethren a hundred and twelve.
11 Sa’an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyatar, firistoci, tare da Uriyel, Asahiya, Yowel, Shemahiya, Eliyel da Amminadab, Lawiyawa.
And David called for Zadok and Abiathar the priests, and for the Levites, for Uriel, Asaiah, and Joel, Shemaiah, and Eliel, and Amminadab,
12 Ya ce musu, “Ku ne kawunan iyalan Lawiyawa; ku da’yan’uwanku Lawiyawa, sai ku tsarkake kanku ku hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila, zuwa wurin da na shirya dominsa.
And said to them, Ye [are] the chief of the fathers of the Levites: sanctify yourselves, [both] ye and your brethren, that ye may bring up the ark of the LORD God of Israel to [the place that] I have prepared for it.
13 Domin ku, Lawiyawa ba ku haura da shi da farko ba ne ya sa Ubangiji Allahnmu ya husata a kanmu. Ba mu tambaye shi game da yadda za mu yi shi a hanyar da aka ƙayyade ba.”
For because ye [did it] not at the first, the LORD our God made a breach upon us, for that we sought him not after the due order.
14 Saboda haka firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu don su hauro da akwatin alkawarin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
So the priests and the Levites sanctified themselves to bring up the ark of the LORD God of Israel.
15 Sai Lawiyawa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah da sanduna a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji.
And the children of the Levites bore the ark of God upon their shoulders with the staffs on it, as Moses commanded, according to the word of the LORD.
16 Dawuda ya faɗa wa shugabannin Lawiyawa su sa’yan’uwansu su zama mawaƙa don su rera waƙoƙi masu farin ciki, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, molaye, garayu da ganguna.
And David spoke to the chief of the Levites to appoint their brethren [to be] the singers with instruments of music, psalteries, and harps, and cymbals, sounding, by lifting up the voice with joy.
17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berekiya daga cikin’yan’uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kushahiya.
So the Levites appointed Heman the son of Joel; and of his brethren, Asaph the son of Berechiah; and of the sons of Merari their brethren, Ethan the son of Kushaiah;
18 Tare da su kuma’yan’uwansa da suke biye bisa ga matsayi. Wato, Zakariya, Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ben, Ma’asehiya, Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom da Yehiyel, matsaran ƙofofi.
And with them their brethren of the second [degree], Zechariah, Ben, and Jaaziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, Eliab, and Benaiah, and Maaseiah, and Mattithiah, and Elipheleh, and Mikneiah, and Obed-edom, and Jeiel, the porters.
19 Mawaƙan nan Heman, Asaf da Etan, ne za su buga kugen tagulla.
So the singers, Heman, Asaph, and Ethan, [were appointed] to sound with cymbals of brass;
20 Zakariya, Aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Unni, Eliyab, Ma’asehiya da Benahiya, ne za su kaɗa molaye masu murya sama-sama, bisa ga alamot.
And Zechariah, and Aziel, and Shemiramoth, and Jehiel, and Unni, and Eliab, and Maaseiah, and Benaiah, with psalteries on Alamoth;
21 Mattitiya, Elifelehu, Miknehiya, Obed-Edom, Yehiyel da Azaziya, ne za su ja garayu masu murya ƙasa-ƙasa bisa ga sheminit.
And Mattithiah, and Elipheleh, and Mikneiah, and Obed-edom, and Jeiel, and Azaziah, with harps on the Sheminith to excel.
22 Kenaniya, shugaban Lawiyawa, shi ne mai bi da waƙoƙi. Wannan hakkinsa ne, gama shi gwani ne a wannan fanni.
And Chenaniah, chief of the Levites, [was] for song: he instructed about the song, because he [was] skillful.
23 Berekiya da Elkana, ne za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
And Berechiah and Elkanah [were] door-keepers for the ark.
24 Shebaniya, Yoshafat, Netanel, Amasai, Zakariya, Benahiya da Eliyezer firistoci, su ne za su busa ƙahoni a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-Edom da Yehiya su ma za su zama masu lura da ƙofofi domin akwatin alkawarin.
And Shebaniah, and Jehoshaphat, and Nethaneel, and Amasai, and Zechariah, and Benaiah, and Eliezer the priests, did blow with the trumpets before the ark of God: and Obed-edom and Jehiah [were] door-keepers for the ark.
25 Sai Dawuda da dattawan Isra’ila da shugabannin ƙungiyoyi dubu suka haura don su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-Edom, da farin ciki.
So David and the elders of Israel, and the captains over thousands, went to bring up the ark of the covenant of the LORD from the house of Obed-edom with joy.
26 Domin Allah ya taimaki Lawiyawan da suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, aka miƙa hadayar bijimai bakwai da raguna bakwai.
And it came to pass, when God helped the Levites that bore the ark of the covenant of the LORD, that they offered seven bullocks and seven rams.
27 To, fa, Dawuda yana saye da kyakkyawar rigar lilin, kamar yadda dukan Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin suka sa, da kuma yadda mawaƙa, da Kenaniya, wanda yake bi da waƙar mawaƙan ya sa. Dawuda kuma ya sa efod lilin.
And David [was] clothed with a robe of fine linen, and all the Levites that bore the ark, and the singers, and Chenaniah the master of the song with the singers: David also [had] upon him an ephod of linen.
28 Sai dukan Isra’ila suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa, da ƙarar ƙahonin raguna da busan ƙahoni, da na ganguna, suna kuma kaɗa molaye da garayu.
Thus all Israel brought up the ark of the covenant of the LORD with shouting, and with sound of the cornet, and with trumpets, and with cymbals, making a noise with psalteries and harps.
29 Yayinda akwatin alkawarin Ubangiji yake shiga Birnin Dawuda, Mikal’yar Shawulu ta leƙa daga taga. Sa’ad da ta ga Sarki Dawuda yana rawa yana shagali, sai ta rena masa wayo a zuciyarta.
And it came to pass, [as] the ark of the covenant of the LORD came to the city of David, that Michal the daughter of Saul, looking out at a window, saw king David dancing and playing: and she despised him in her heart.

< 1 Tarihi 15 >