< 1 Tarihi 14 >

1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
Un Īrams, Tirus ķēniņš, sūtīja vēstnešus pie Dāvida un ciedru kokus un mūrniekus un būvmeistarus, viņam uztaisīt namu.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
Un Dāvids manīja, ka Tas Kungs viņu bija apstiprinājis par ķēniņu pār Israēli; jo viņa valstība tapa varen paaugstināta viņa Israēla ļaužu labad.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
Un Dāvids ņēma vēl vairāk sievu Jeruzālemē un Dāvidam dzima vēl vairāk dēlu un meitu.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Un šie ir to bērnu vārdi, kas viņam piedzima Jeruzālemē: Šamuūs un Zobabs, Nātans un Salamans.
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
Un Jebears un Elizuūs un Elvalets
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
Un Nogus un Nevegs un Japius
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
Un Elišamus un BaelJadus un Elivalets.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
Kad nu Fīlisti dzirdēja, ka Dāvids bija svaidīts par ķēniņu pār visu Israēli, tad visi Fīlisti nāca, Dāvidu meklēt. Un kad Dāvids to dzirdēja, tad viņš tiem izgāja pretī.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
Un Fīlisti nāca un izplētās Refaīm ielejā.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
Tad Dāvids vaicāja Dievam un sacīja: vai man būs iet pret Fīlistiem, un vai tu tos dosi manā rokā? Un Tas Kungs tam sacīja: celies, jo es tos došu tavā rokā.
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Un tie gāja uz BaālPracim, un Dāvids tos tur sakāva, un Dāvids sacīja: Dievs aizrāvis manus ienaidniekus caur manu roku, tā kā ūdens rauj. Tādēļ tie nosauca to vietu BaālPracim (rāveju vieta).
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
Un tie tur pameta savus dievus; un Dāvids pavēlēja, tos sadedzināt ar uguni.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
Bet Fīlisti atkal nāca un apmetās ielejā.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
Tad Dāvids atkal vaicāja Dievam, un Dievs uz to sacīja: neej aiz viņiem bet ej apkārt ap viņiem, un ej tiem virsū pret tiem raudu kokiem.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
Un kad tu dzirdēsi soļus rībam raudu koku galotnēs, tad izej uz kaušanos, jo Dievs iziet tavā priekšā, kaut Fīlistu karaspēku.
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
Un Dāvids darīja, kā Dievs tam bija pavēlējis; un tie kāva Fīlistu karaspēku no Gibeonas līdz Gazerai.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
Tā Dāvida slava izpaudās pa visām zemēm, un Tas Kungs lika bailēm no viņa uziet visiem pagāniem.

< 1 Tarihi 14 >