< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Então todo o Israel se ajuntou a David em Hebron, dizendo: Eis que somos teus ossos e tua carne.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
E também já de antes, sendo Saul ainda rei, eras tu o que fazias sair e entrar a Israel: também o Senhor teu Deus te disse: Tu apascentarás o meu povo Israel, e tu serás chefe sobre o meu povo Israel.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Também vieram todos os anciãos de Israel ao rei, a Hebron, e David fez com eles aliança em Hebron, perante o Senhor: e ungiram a David rei sobre Israel, conforme a palavra do Senhor pelo ministério de Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
E partiu David e todo o Israel para Jerusalém, que é Jebus: porque ali estavam os jebuseus, moradores da terra.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
E disseram os moradores de Jebus a David: Tu não entrarás aqui. Porém David ganhou a fortaleza de Sião, que é a cidade de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Porque disse David: Qualquer que primeiro ferir os jebuseus será chefe e maioral. Então Joab, filho de Zeruia, subiu primeiro a ela; pelo que foi feito chefe.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
E David habitou na fortaleza; pelo que se chamou a cidade de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
E edificou a cidade ao redor, desde milo até ao circuito: e Joab renovou o resto da cidade.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
E ia-se David cada vez mais aumentando e crescendo; porque o Senhor dos exércitos era com ele.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
E estes foram os chefes dos varões que David tinha, e que o apoiaram fortemente no seu reino, com todo o Israel, para o fazerem rei, conforme a palavra do Senhor, tocante a Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
E estes foram do número dos varões que David tinha: Jasobeam, hachmonita, o principal dos capitães, o qual, brandindo a sua lança contra trezentos, de uma vez os matou.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
E, depois dele, Eleazar, filho de Dodó, o ahohita: ele estava entre os três varões.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Este esteve com David em Pas-dammim, quando os philisteus ali se ajuntaram à peleja, e o pedaço de campo estava cheio de cevada: e o povo fugiu de diante dos philisteus.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
E puseram-se no meio daquele pedaço, e o defenderam, e feriram os philisteus; e obrou o Senhor um grande livramento.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
E três dos trinta chefes desceram à penha, a David, na caverna de Adullam: e o arraial dos philisteus estava acampado no vale de Rephaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
E David estava então no lugar forte: e o alojamento dos philisteus estava então em Beth-lehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
E desejou David, e disse: Quem me dará a beber da água do poço de Beth-lehem, que está junto à porta?
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Então aqueles três romperam pelo arraial dos philisteus, e tiraram água do poço de Beth-lehem, que estava à porta, e tomaram dela, e a trouxeram a David; porém David não a quis beber, mas a derramou ao Senhor,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
E disse: Nunca meu Deus permita que faça tal! beberia eu o sangue destes varões com as suas vidas? Pois com perigo das suas vidas a trouxeram. E ele não a quis beber: isto fizeram aqueles três varões.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
E também Abisai, irmão de Joab, foi chefe de três, o qual, brandindo a sua lança contra trezentos, os feriu: e teve nome entre os três.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Dos três foi mais ilustre do que os outros dois, pelo que foi chefe deles; porém não chegou aos primeiros três.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Também Benaias, filho de Joiada filho de um valente varão, grande em obras, de Kabseel: ele feriu a dois fortes leões de Moab; e também desceu, e feriu um leão dentro de uma cova, no tempo da neve.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Também feriu ele a um homem egípcio, homem de grande altura, de cinco côvados: e trazia o egípcio uma lança na mão, como o órgão do tecelão; mas desceu contra ele com uma vara, e arrancou a lança da mão do egípcio, e o matou com a sua própria lança
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Estas coisas fez Benaias, filho de Joiada; pelo que teve nome entre aqueles três varões.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Eis que dos trinta foi ele o mais ilustre; contudo não chegou aos três: e David o pôs sobre os da sua guarda.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
E foram os varões dos exércitos: Asael, irmão de Joab, Elhanan, filho de Dodo, de Beth-lehem,
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Sammoth, o harodita, Heles, o pelonita,
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, filho de Ikkes, o tekoita, Abiezer, o anathothita,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbechai, o husathita, Ilai, o ahohita,
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharai, o netophathita, Heled, filho de Baena, o netophathita,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithai, filho de Ribai, de Gibeah, dos filhos de Benjamin, Benaias, o pirathonita,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai, do ribeiro de Gaas, Abiel, o arbathita,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Asmaveth, o baharumita, Eliahba, o saalbonita.
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Dos filhos de Hasem, o gizonita: Jonathan, filho de Sage, o hararita,
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam, filho de Sachar, o hararita, Eliphal, filho de Ur,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hepher, o mecheratita, Ahias, o pelonita,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hesro, o carmelita, Naari, filho d'Esbai,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, irmão de Nathan, Mibhar, filho de Geri,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zelek, o amonita, Nahrai, o berothita, escudeiro de Joab, filho de Zeruia,
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, o ithrita, Gareb, o ithrita,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urias, o hethita, Zabad, filho de Ahlai,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, filho de Siza, o rubenita, chefe dos rubenitas; todavia sobre ele havia trinta;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanam, filho de Maacha, e Josaphat, o mithnita,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzias, o astharathita, Sama e Jeiel, filhos de Hotham, o aroerita,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, filho de Simri, e Joha, seu irmão, o tisita,
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel, o mahavita, e Jeribai, e Joshavias, filhos d'Elnaam, e Ithma, o moabita,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, e Obed, e Jaasiel, e Mesobaia.

< 1 Tarihi 11 >